• English
  • Business News
Thursday, October 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwalliya A Cikin Gida

by Bilkisu Tijjani
2 years ago
Kwalliya

Assalamu alaikum masu karatu, barkammu da sake haduwa da ku a wannan makon a cikin shirin namu mai farin jini da albarka na Uwargida Sarautar Mata.

A yau shafin namu zai tabo mana kwalliyar uwargida a cikin gidanta:

Kwalliya wata aba ce da take kara wa mace kyau duk kyan mace idan ta yi kwalliya za ta kara kyau idan wadda tasaba da kwalliyar ce daidai da rana daya idan ba ta yi ba sai an ganta wata iri, haka zalika duk munin mace idan ta yi kwalliya  za ta yi kyau saboda haka kwalliya tana daya daga cikin babban abu na gyaran mace.

Uwargida mu daure muna kwalliya a cikin gidammu na aure sai ki ga idan mace ta yi aure wai shike nan ta bar kwalliya kullum idan ka shiga gidanta kamar an tono ta a rami wai ita matar aure. Za ki ga da kafin ta yi aure ita uwar kwalliya ce har ma da kayan kwalliya take yawo a cikin jaka a jima a goga, amma ta yi aure ta bari maimakon a ce ai yanzu ne ma za’a fara kwalliya tun da kin yi aure kina da wanda za ki yi wa ya gan ki ya ji dadi ki samu lada ki yi wadda tafi tada lokacin yana zuwa zance.

Kwalliya ido ce ga mace kwalliya tana gyara mace tana kara wa mace daraja da kima a idon maigida.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Za A Magance Amosanin Baki

Hadin Tsumin Baure

Amma sai ki ga matar aure in an ganta da kwalliya to fita za ta yi shi ne za ta yi kwalliya har sai ki ji yara daga sun ganta da kwalliya suna cewa mama za ki biki ne? wato fita za ta yi shi ne ta yi kwalliya.

Akwai wani kuskure da muke yi wai ba ya yaba kwalliya ta shi ya sa ba zan yi ba, tabbas akwai zafi ki dage ki takarkare ki bata kusan awa daya kina yi wa maigida kwalliya amma sai ki ga wani idan ya shigo ko kallon inda kike ba zai yi ba, ballantana ya ce kin yi kyau wannan kalmar tana yi wa maza nauyi a baki, sannan kuma gaskiya da ciyo. To amma me kar ki damu da sai ya yaba ki ke kanki kin ji dadin kin yi kyau, sannan kuma ko gaban madubi kika je kin san kin yi kyau, to wannan ya kara miki karfin gwiwar yi, shima kansa ya ji dadi ya san kin yi kyau kawai ya budi baki ne ya ce kin yi kyau yake masa nauyi idan kin ga kin yi kyau wannan ya kara miki karfin gwiwar gobe ma ki sake wadda tafi wannan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Za A Magance Amosanin Baki
Ado Da Kwalliya

Yadda Za A Magance Amosanin Baki

October 4, 2025
Hadin Tsumin Baure
Ado Da Kwalliya

Hadin Tsumin Baure

September 27, 2025
Gyaran fuska
Ado Da Kwalliya

Gyaran Fuska Da Laushin Fata

August 30, 2025
Next Post
Matsalolin Da Ke Faruwa Tsakanin Mata Masu Aiki Da Mazajensu

Matsalolin Da Ke Faruwa Tsakanin Mata Masu Aiki Da Mazajensu

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Diflomasiyyar Shugabanni Na Matukar Taka Rawar Gani Wajen Jagorantar Dangantakar Sin Da Amurka

October 22, 2025
Majalisar NUJ Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

Majalisar NUJ Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

October 22, 2025
Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

October 22, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Cafke Wani Matashi Ɗan Shekara 15 Da Ake Zargi Da Yin Fashi Da Makami A Gombe

October 22, 2025
Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera

Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera

October 22, 2025
An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

October 22, 2025
Adadin Yawon Shakatawa Da Mutanen Sin Suka Yi A Cikin Gida Ya Zarce Biliyan 4.998 Tsakanin Janairu Da Satumban Bana

Adadin Yawon Shakatawa Da Mutanen Sin Suka Yi A Cikin Gida Ya Zarce Biliyan 4.998 Tsakanin Janairu Da Satumban Bana

October 22, 2025
Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina

Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina

October 22, 2025
Kasar Sin Ta Sake Farfado Da Muhimman Koguna Da Tafkuna 88 A Kokarin Inganta Muhalli

Kasar Sin Ta Sake Farfado Da Muhimman Koguna Da Tafkuna 88 A Kokarin Inganta Muhalli

October 22, 2025
Tanka

Majalisa Ta Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Kai Agajin Gaggawa Ga Waɗanda Fashewar Tanka Ta Shafa A Neja

October 22, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.