Kwanan baya, kwamitin kolin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin ya shirya taron bita tare da wadanda ba ’yan jam’iyyar ba, dangane da yanayin tattalin arzikin kasar, da kuma ayyukan tattalin arziki da za a aiwatar a rabin shekarar bana ta biyu, domin sauraren ra’ayoyinsu.
Xi Jinping, babban sakataren jam’iyyar ne ya shugabanci taron tare da ba da muhimmin jawabi, inda ya ce, dole ne a zage damtse wajen gudanar da ayyukan tattalin arziki a rabin shekarar bana ta biyu, kuma a tabbatar da gudanar da ayyukan ba tare da tangarda ba, kana a aiwatar da cikakken sabon tunanin raya kasa daga dukkan fannoni, da gaggauta kafa tsarin raya kasa, da kiyaye aiwatar da manufofi ba tare da matsala ba, da inganta aiwatar da manufofi tare da yin hangen nesa da sanin ya kamata.
Shugaban na Sin ya ce, ya zama wajabi a mayar da muhimmanci ga samar da guraben aikin yi, da kwantar da hankulan kamfanoni, da tafiyar da harkokin kasuwanci, da samar da tabbaci game da hasashen da ake yi kan tattalin arziki, da karfafa sayayya, da dakatar da yin takara maras dacewa, da kawar da cikas a kasuwar gida, da rungumar wani sabon tsarin ci gaba mai “zagaye biyu”, wato wanda zai tanadi amfani da kasuwar gida a matsayin jigo, tare da barin kasuwannin gida da na waje su karfafi junansu, a kokarin cimma manufar raya tattalin arziki, da zamantakewar al’ummar kasar a bana, da samun nasarar kammala shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar karo na 14. (Tasallah Yuan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp