• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwamoti B Laori Ya Kaddamar Da Zauren Taro a Borrong, Demsa

byMuh'd Shafi'u Saleh
2 years ago
Kwamoti

A wani gagarumin biki, dan majalisar mai wakiltar mazabun kananan hukumomin Demsa, Numan da Lamurde a majalisar wakilai ta kasa Honarabul Kwamoti La’ori, ya kaddamar da wani dakin taro da ya yiwa lakabi da Waziri Mbula, Chief John Eddy Manassa.

Da yake jawabi a taron, dan majalisar ya jinjinawa marigayi Waziri Mbula bisa kokarin da ya yi na hada kan jama’a, ya kuma yi addu’ar Allah ya sa ya ci gaba da zama alamar hadin kai, fahimtar juna da samar da zaman lafiya ga al’ummar yankin.

  • Kotun Koli Za Ta Saurari Shari’ar Zaben Gwamnan Adamawa A Ranar Litinin 
  • Kisan Budurwa: Gwamnatin Adamawa Za Ta Rufe Otal 70

Haka kuma ya bayyana cewa, a wani taro da aka yi a dakin taro na Prince Medan Teneke da ya gina a garin Demsa ne wasu daga mazabun suka nemi da ya gina musu ajujuwa da ya gina a Lasala, Unguwar Gwamba; Zauren jarrabawar JJ Fwa da ke gundumar Mbula, da kuma zauren John Eddy Manassa da aka kaddamar a Borrong ranar Asabar.

Don haka ya ja hankalin al’ummar mazabar da su ci gaba da tuntubarshi da maganganu masu ma’ana da kuma ra’ayoyin da za su ciyar da al’ummar mazabarsa gaba tare da tabbatar musu da cewa kunnuwansa a kowane lokaci a bude suke.

Baya ga ci gaban da aka samu wanda ya shafi mazaba a daukacin sassan mazabarsa, dan majalisar ya aiwatar da ayyukan more rayuwa daban-daban a fannin ilimi, kiwon lafiya, samar da wutar lantarki, ruwan sha da sauran muhimman sassa a kusan kashi 90% na mazabun 30 dake kananan hukumomin Demsa, Numan da Lamurde, a karamar hukumar Demsa, mazabar Dilli ta rage bai kai ga kammala aikin ba.

LABARAI MASU NASABA

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

Da itama ke jawabi kafin kaddamar da zauren taron, mataimakiyar gwamnan jihar Farfesa Kaletapwa George Farauta, ta yabawa dan majalisar bisa yadda ya dinke baraka da samar da ababen more rayuwa a mazabarsa, inda ta yi kira ga jama’a da su kula da zauren da za su rika gudanar da tarurrukan bita, liyafar aure da sauran muhimman tarukan zamantakewa a yankin.

Cikin manyan bakin da suka samu halartar taron sun hada da ‘yar majalisa mai wakiltar karamar hukumar Demsa a majalisar dokokin jihar Adamawa kuma shugaban masu rinjaye na majalisar Hon. Kate Mamuno, da dan majalisar mai wakiltar karamar hukumar Numan a majalisar dokokin jihar Hon. Pwamwakaino Makondo.

Shugabannin kananan hukumomin Numan, Demsa da Lamurde, Hon. Da kyar Dilli, Barr. John Tunor, Hon. Happy Maxwell, Barr Leader Teneke, Hon. Elkanah Kados, Hon. A.A Sadat, Hon. Satina, Cif Niwesa George, Dr. Ben Direi, Hon. Malena John Manassa, da ɗimbin abokan siyasa da masu ruwa da tsaki da yawa da ba za su ambatu ba.

Muhimman abubuwan da suka faru a taron sun hada da faretin ’yan wasan gargajiya daga al’ummomin masarautar Mbula. Mahayin dawakai da yawan gabatarwa a cikin wakoki da kasidu.

Murum Mbula, wanda ya karbi manya mutane a fadarsa ya samu wakilcin Cif Lawsom Gadiel, Hakimin Borrong a taron.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Next Post
Bankunan Kasashen Ketare Sun Yaba Da Bunkasuwar Tattalin Arzikin Kasar Sin

Bankunan Kasashen Ketare Sun Yaba Da Bunkasuwar Tattalin Arzikin Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version