• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwangilar Biliyan 30: PDP Ta Bukaci EFCC Ta Binciki Gwamnatin Sakkwato

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto and Sulaiman
12 months ago
in Labarai
0
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar PDP a jihar Sakkwato ta bukaci Hukumomin Yaki da Cin Hanci da Rashawa na EFCC da ICPC da su binciki kwangilar sanya raga a titunan birnin Sakkwato da gwamnati ta bayar kan naira biliyan 30.

 

Jam’iyyar ta bayyana cewar, aikin asarar kudin jama’a ne domin ba ya da tasiri ga rayuwar al’umma, don haka, ta bukaci binciken gaggawa kan yadda gwamnatin Sakkwato ke kashe kudaden al’umma.

  • Mene Ne Dalilin Da Ya Sa Kamfanonin Waje Su Zuba Jari Ga Kasar Sin?
  • ‘Yan Nijeriya Na Cikin Matsi Saboda Hauhawar Farashin Kayayyaki – Abdulsalami

A jawabin da jam’iyyar ta fitar a ranar Laraba wanda kakakinta, Hassan Sahabi Sanyinnawal ya sanyawa hannu, jam’iyyar ta bayyana cewa, a shirye take ta fuskanci ko wane irin bincike kan ayyukan da gwamnatin Tambuwal ta aiwatar.

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Jam’iyyar ta bayyana cewa, a shirye tsohon Gwamnan, da ‘yan majalisar zartaswarsa da manyan jami’an gwamnatinsa suke, su bayyana a gaban hukumar binciken a duk lokacin da aka bukata.

 

Kiran EFCC da ICPC su gudanar da binciken, ya biyo baya ne a yayin da gwamnatin jihar ta gabatar da takardar korafi ga hukumar da ta kafa kwamitiin binciken tsohuwar gwamnatin jihar kan zargin karkatar da hannun jari na naira biliyan 16 da gwamnatin Tambuwal ta yi.

 

A sanarwar, jam’iyyar ta zargi gwamna Ahmed Aliyu da almubbazaranci ta hanyar kashe biilyoyin kudade a ayyukan da ba su da muhimmanci kamar zagaye tituna da waya a daidai lokacin da jama’a ke cikin halin kunci da tsadar rayuwa.

 

Haka ma jam’iyyar ta bayyana cewa, a yayin da al’ummar jihar ke cike da mamaki da kaduwa kan kwangilar gyaran rijiyoyin burtsatse 25 kan naira biliyan 1.2 sai ga batun naira biliyan 30 na zagaya tituna da raga.

 

Jawabin ya ce, gwamnatin jihar ta na kokarin karkatar da hankalin jama’a ne kan gazawar gwamnatinsu ta hanyar zarge- zargen da ba su da tushe ga gwamnatin Tambuwal wanda jam’iyyar ta bayyana cewa, gwamnati ce mafi aiwatar da gaskiya da adalci wadda cibiyoyin bin diddigin ayyukan gwamnati na duniya suka tabbatar.

 

“Ayyukan gyaran sha-tale-tale da hanyoyin ratsewa da gwamnati ta bayar, ba a bi ka’idojin bayar da kwangila ba, domin an bayar da aikin ba tare da amincewar majalisar zartaswar gwamnati ba, ba kuma tare da cike ka’idoji ba.”

 

“A kan wannan, muna kira ga hukumomin EFCC da ICPC da su gudanar da cikakken bincike kan kwangilar biliyan 30 ta zagaya tituna da raga domin tabbatar da gaskiya da adalci ga al’ummar jihar Sakkwato.” In ji Jam’iyyar


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: EFCCGwamnatin SakkwatoICPC
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mene Ne Dalilin Da Ya Sa Kamfanonin Waje Su Zuba Jari Ga Kasar Sin?

Next Post

Dakta Gadan-ƙaya Ya Bada Haƙuri Kan Zargin Auren Jinsi Da Ya Yi A Bauchi

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

5 hours ago
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 
Labarai

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

6 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

8 hours ago
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

10 hours ago
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

12 hours ago
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
Labarai

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

13 hours ago
Next Post
Dakta Gadan-ƙaya Ya Bada Haƙuri Kan Zargin Auren Jinsi Da Ya Yi A Bauchi

Dakta Gadan-ƙaya Ya Bada Haƙuri Kan Zargin Auren Jinsi Da Ya Yi A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.