• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwangilar Biliyan 30: PDP Ta Bukaci EFCC Ta Binciki Gwamnatin Sakkwato

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto and Sulaiman
1 year ago
PDP

Jam’iyyar PDP a jihar Sakkwato ta bukaci Hukumomin Yaki da Cin Hanci da Rashawa na EFCC da ICPC da su binciki kwangilar sanya raga a titunan birnin Sakkwato da gwamnati ta bayar kan naira biliyan 30.

 

Jam’iyyar ta bayyana cewar, aikin asarar kudin jama’a ne domin ba ya da tasiri ga rayuwar al’umma, don haka, ta bukaci binciken gaggawa kan yadda gwamnatin Sakkwato ke kashe kudaden al’umma.

  • Mene Ne Dalilin Da Ya Sa Kamfanonin Waje Su Zuba Jari Ga Kasar Sin?
  • ‘Yan Nijeriya Na Cikin Matsi Saboda Hauhawar Farashin Kayayyaki – Abdulsalami

A jawabin da jam’iyyar ta fitar a ranar Laraba wanda kakakinta, Hassan Sahabi Sanyinnawal ya sanyawa hannu, jam’iyyar ta bayyana cewa, a shirye take ta fuskanci ko wane irin bincike kan ayyukan da gwamnatin Tambuwal ta aiwatar.

 

LABARAI MASU NASABA

COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

Jam’iyyar ta bayyana cewa, a shirye tsohon Gwamnan, da ‘yan majalisar zartaswarsa da manyan jami’an gwamnatinsa suke, su bayyana a gaban hukumar binciken a duk lokacin da aka bukata.

 

Kiran EFCC da ICPC su gudanar da binciken, ya biyo baya ne a yayin da gwamnatin jihar ta gabatar da takardar korafi ga hukumar da ta kafa kwamitiin binciken tsohuwar gwamnatin jihar kan zargin karkatar da hannun jari na naira biliyan 16 da gwamnatin Tambuwal ta yi.

 

A sanarwar, jam’iyyar ta zargi gwamna Ahmed Aliyu da almubbazaranci ta hanyar kashe biilyoyin kudade a ayyukan da ba su da muhimmanci kamar zagaye tituna da waya a daidai lokacin da jama’a ke cikin halin kunci da tsadar rayuwa.

 

Haka ma jam’iyyar ta bayyana cewa, a yayin da al’ummar jihar ke cike da mamaki da kaduwa kan kwangilar gyaran rijiyoyin burtsatse 25 kan naira biliyan 1.2 sai ga batun naira biliyan 30 na zagaya tituna da raga.

 

Jawabin ya ce, gwamnatin jihar ta na kokarin karkatar da hankalin jama’a ne kan gazawar gwamnatinsu ta hanyar zarge- zargen da ba su da tushe ga gwamnatin Tambuwal wanda jam’iyyar ta bayyana cewa, gwamnati ce mafi aiwatar da gaskiya da adalci wadda cibiyoyin bin diddigin ayyukan gwamnati na duniya suka tabbatar.

 

“Ayyukan gyaran sha-tale-tale da hanyoyin ratsewa da gwamnati ta bayar, ba a bi ka’idojin bayar da kwangila ba, domin an bayar da aikin ba tare da amincewar majalisar zartaswar gwamnati ba, ba kuma tare da cike ka’idoji ba.”

 

“A kan wannan, muna kira ga hukumomin EFCC da ICPC da su gudanar da cikakken bincike kan kwangilar biliyan 30 ta zagaya tituna da raga domin tabbatar da gaskiya da adalci ga al’ummar jihar Sakkwato.” In ji Jam’iyyar

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 
Labarai

COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

October 29, 2025
Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci
Manyan Labarai

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

October 29, 2025
Gwamnatin Rikon Kwarya: Shirin DSS Ne Na Damke Atiku Da Peter Obi Kafin Rantsar Da Tinubu
Labarai

DSS Ta Kama Wani Matashi Da Ya Yi Kira A Yi Juyin Mulki A Kafofin Sada Zumunta

October 29, 2025
Next Post
Dakta Gadan-ƙaya Ya Bada Haƙuri Kan Zargin Auren Jinsi Da Ya Yi A Bauchi

Dakta Gadan-ƙaya Ya Bada Haƙuri Kan Zargin Auren Jinsi Da Ya Yi A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

October 29, 2025
Binciken ‘Yan Sanda Kan Wanda Ake Zargi Da Tawayen “‘Yancin Kan Taiwan” Mataki Ne Na Adalci Don Kare Hadin Kan Kasa

Binciken ‘Yan Sanda Kan Wanda Ake Zargi Da Tawayen “‘Yancin Kan Taiwan” Mataki Ne Na Adalci Don Kare Hadin Kan Kasa

October 29, 2025
Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

October 29, 2025
Xi Jinping Zai Gana Da Donald Trump

Xi Jinping Zai Gana Da Donald Trump

October 29, 2025
Gwamnatin Rikon Kwarya: Shirin DSS Ne Na Damke Atiku Da Peter Obi Kafin Rantsar Da Tinubu

DSS Ta Kama Wani Matashi Da Ya Yi Kira A Yi Juyin Mulki A Kafofin Sada Zumunta

October 29, 2025
An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

October 29, 2025
Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

October 29, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Tsoron Boko Haram Ne Ya Sa Jonathan Ya Fasa Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II

October 29, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.