ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dakta Gadan-ƙaya Ya Bada Haƙuri Kan Zargin Auren Jinsi Da Ya Yi A Bauchi

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
2 years ago
Auren jinsi

Fitaccen malamin addinin musulunci da ke jihar Kano, Dakta Abdallah Gadon-Ƙaya ya yi amai ya lashe kan zargin da ya yi na cewa, wasu gungun masu auren jinsi da luwaɗi da maɗigo sun taru a jihar Bauchi domin sheƙe ayarsu a kwanakin baya.

 

Malamin ya fito ɓalo-ɓalo ya janye kalamansa tare da bai wa al’umma musamman musulmai haƙuri bisa furucin nasa.

ADVERTISEMENT
  • Kwangilar Biliyan 30: PDP Ta Bukaci EFCC Ta Binciki Gwamnatin Sakkwato
  • Ambaliyar Ruwa Ta Katse Hanyar Maiduguri Zuwa Damboa

Gadon-Kaya ya ce, bisa zurfafa bincike da gwamnatin jihar Bauchi da hukumomin tsaro suka yi, an tabbatar da cewa labarin da ya bayar ƙarya ce sam babu wani auren jinsi da aka taru daga jihohi domin yinsa a jihar Bauchi.

 

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Idan za a tuna dai malamin ya taɓa shelanta wa duniya cewa, wani mutumi ya kirasa ya tabbatar masa da cewa, ana auren jinsi da luwaɗi da maɗigo a wani otel da ke jihar Bauchi. Malamin har ya ce yana da hujja da sunan otel ɗin kuma zai iya bayarwa idan aka nema.

 

Sai dai bayan da gwamnatin jihar Bauchi ta hannun hukumar Shari’a da ta nemi malamin domin ya zo ya gabatar mata da hujjojin nasa da kuma inda abun ya faru sai ya janye kalaman nasa.

 

Kan hakan ne malamin ya fito cikin wani faifayin bidiyo mai tsawon mintuna fiye da biyar ya na bai wa gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad da jami’an gwamnatin da hukumomin tsaro haƙuri bisa bayanin da ya fitar da ya tada hankalin jama’a da daman gaske.

 

Ya ce: “A satukan da suka gabata, akwai bayanin da na yi a kan labari da wani bawan Allah ya ba ni a kan faruwar wani taron auren jinsi a jihar Bauchi. Na ce ya kirani ya bani bayani cewa ga abun da ke faruwa cewa a yi wa’azi a faɗakar kuma a yi bincike.

 

“To, mun yi wannan maganar kuma maganar ta yaɗu kuma muka ce a bincika hukuma ta ɗauki mataki. Hukuma ta bincika, jami’an tsaro sun bincika babu wannan auren jinsin kuma ba a yi shi ba a jihar Bauchi.”

 

Ya ce suna godiya wa Allah bisan rashin faruwar hakan,  domin a cewarsa, hakan ma alkairi ne domin ba a samu faruwar ɓarnar ba.

 

Ya jinjina wa irin ƙoƙarin da jami’an tsaro da gwamnatin jihar Bauchi suka yi wajen bincikawa sosai har suka tabbatar da babu faruwar wannan labarin kwata-kwata.

 

Ya nuna cewa, a sakamakon kalaman nasa, rayukan dubban mutane sun ɓaci musamman wadanda suke kishin musulunci a ko’ina suke.

 

“Don haka, muna amfani da wannan damar tun da bincike ya tabbatar da ba a yi wannan abun ba, muna bada haƙuri ga duk wanda wannan abun ya shafe shi tun daga kan mai girma gwamna a matsayinsa na uba kuma jagora a wannan jihar da sauran muƙarrabansa da na kusa da shi, da jami’an tsaro da dukkan sauran al’umma baki daya.

 

“Mu yi haƙuri dukkanmu. Saboda ita da’awar haka ta gada wani lokacin za a iya faɗan wani abun wani lokacin ya zama haka ne wani lokacin ya zama ba haka ba ne, to daman ba fata muke abun ya faru ba. Allah ya bai wa kowa haƙuri baki ɗayanmu, Allah ya sa muma mu dace.

 

“Allah shi ne shaida ba mun yi wannan abun saboda cin zarafi ko ɓata wani ko kuma cin mutuncin wani, kwata-kwata babu wannan a tare da mu. Wallahi kishin jihar ce. Ni ɗan Bauchi ne, halastaccen ɗan Bauchi. Zan iya bayar da duk abun da na mallaka da rayuwata don na kare wannan jihar tawa na taimaki addini na taimaki da’awa.”

Auren jinsi
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba
Auren jinsi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Gwamnan Kano Ya Rushe Kantomomin Kananan Hukumomin Jihar Kano 44

Gwamnan Kano Ya Rushe Kantomomin Kananan Hukumomin Jihar Kano 44

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.