• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Yaba Wa ‘Yan Jarida Bisa Yada Ayyukan Hukumar

by yahuzajere
2 years ago
in Labarai
0
NIS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanturolan Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS), a Jihar Ribas, James Sunday, ya yaba wa ‘yan jarida bisa yadda suke yada ayyukan da hukumar take gudanarwa a cikin kasa da waje.

Kwanturolan wanda ya kasance tsohon jami’in hulda da jama’a na hukumar ya ce a matsayin ‘yan jarida na abokan aiki tare da kawo ci gaba, wajibi ne ya taya su murnar bikin ranarsu wanda aka yi na bana a ranar Laraba 3 ga watan Mayun 2023.

  • Rukunin Farko Na ‘Yan Nijeriya 376 Da Aka Kwaso A Sudan Sun Iso Abuja

Sanarwar da ta fito daga ofishin NIS na Jihar Ribas, ta ce Sunday James ya kuma yi jinjina a kan yadda ‘yan jarida ke wayar da kan jama’a domin su fahimci hakkokinsu na kasa da kuma gudunmawar da ya kamata su bayar wajen gina kasa.

Ya kara da cewa, hukumar ta NIS a Jihar Ribas ta samu kwarin gwiwa wajen bayar da rahoton nasarorin da take samu tare da inganta ayyukanta da take gudanarwa domin ‘yan kasa.

Kwanturolan ya kuma yi amfani da wannan dama ta bikin ranar ‘yan jaridan wajen yaba wa Kwanturola Janar na NIS, Isa Jere Idris, MFR, saboda mutuntawa da hakurin da yake da shi da girmama ‘yancin ‘yan jarida da kuma jajircewarsa na yin aiki tare da kafafen yada labarai a matsayin abokan hadin gwiwa na kawo ci gaba.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

Ya ba da misalin cewa, kasancewar Kwanturola Janar Jere, ya yi karatunsa na jami’a ne a fannin nazarin sadarwa, hakan ya kara kyautata alakarsa da ‘yan jarida wanda suke samun hadin kansa a duk lokacin da suka zo neman bayani ko Karin haske game da ayyukan da NIS take gudanarwa tun daga lokacin da ya kama aiki a matsayin shugaban hukumar.

Kwanturola James, ya ce ‘yan jarida na da kyakkyawar alaka, hadin gwiwa, da ‘yanci wajen samun bayanan da za su bukata ba tare da kawo cikas ga tsaron kasa daga NIS ba.

Ya kuma hori ‘yan jarida da su kasance masu adalci da kuma da’a ga aikinsu yayin da suke farauto labarai ko tattaunawa da jama’a domin ilmantar da ‘yan kasa. Kana ya hore su a koyaushe su yi kokarin inganta aikinsu tare da kawo sabon salo irin na ci gaban zamani, kana ya ba ta tabbacin NIS za ta ci gaba da kyautata alaka da ‘yan jarida a koyaushe a matsayinsu na abokan aiki.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rukunin Farko Na ‘Yan Nijeriya 376 Da Aka Kwaso A Sudan Sun Iso Abuja

Next Post

Hukumar NDE Ta Fara Rajistar Marasa Aiki A Sakkwato

Related

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano
Labarai

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

1 hour ago
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Labarai

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

2 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

6 hours ago
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace
Labarai

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

7 hours ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

16 hours ago
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta
Labarai

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

18 hours ago
Next Post
Hukumar NDE Ta Fara Rajistar Marasa Aiki A Sakkwato

Hukumar NDE Ta Fara Rajistar Marasa Aiki A Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.