• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Yaba Wa ‘Yan Jarida Bisa Yada Ayyukan Hukumar

by yahuzajere
2 years ago
in Labarai
0
NIS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanturolan Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS), a Jihar Ribas, James Sunday, ya yaba wa ‘yan jarida bisa yadda suke yada ayyukan da hukumar take gudanarwa a cikin kasa da waje.

Kwanturolan wanda ya kasance tsohon jami’in hulda da jama’a na hukumar ya ce a matsayin ‘yan jarida na abokan aiki tare da kawo ci gaba, wajibi ne ya taya su murnar bikin ranarsu wanda aka yi na bana a ranar Laraba 3 ga watan Mayun 2023.

  • Rukunin Farko Na ‘Yan Nijeriya 376 Da Aka Kwaso A Sudan Sun Iso Abuja

Sanarwar da ta fito daga ofishin NIS na Jihar Ribas, ta ce Sunday James ya kuma yi jinjina a kan yadda ‘yan jarida ke wayar da kan jama’a domin su fahimci hakkokinsu na kasa da kuma gudunmawar da ya kamata su bayar wajen gina kasa.

Ya kara da cewa, hukumar ta NIS a Jihar Ribas ta samu kwarin gwiwa wajen bayar da rahoton nasarorin da take samu tare da inganta ayyukanta da take gudanarwa domin ‘yan kasa.

Kwanturolan ya kuma yi amfani da wannan dama ta bikin ranar ‘yan jaridan wajen yaba wa Kwanturola Janar na NIS, Isa Jere Idris, MFR, saboda mutuntawa da hakurin da yake da shi da girmama ‘yancin ‘yan jarida da kuma jajircewarsa na yin aiki tare da kafafen yada labarai a matsayin abokan hadin gwiwa na kawo ci gaba.

Labarai Masu Nasaba

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Ya ba da misalin cewa, kasancewar Kwanturola Janar Jere, ya yi karatunsa na jami’a ne a fannin nazarin sadarwa, hakan ya kara kyautata alakarsa da ‘yan jarida wanda suke samun hadin kansa a duk lokacin da suka zo neman bayani ko Karin haske game da ayyukan da NIS take gudanarwa tun daga lokacin da ya kama aiki a matsayin shugaban hukumar.

Kwanturola James, ya ce ‘yan jarida na da kyakkyawar alaka, hadin gwiwa, da ‘yanci wajen samun bayanan da za su bukata ba tare da kawo cikas ga tsaron kasa daga NIS ba.

Ya kuma hori ‘yan jarida da su kasance masu adalci da kuma da’a ga aikinsu yayin da suke farauto labarai ko tattaunawa da jama’a domin ilmantar da ‘yan kasa. Kana ya hore su a koyaushe su yi kokarin inganta aikinsu tare da kawo sabon salo irin na ci gaban zamani, kana ya ba ta tabbacin NIS za ta ci gaba da kyautata alaka da ‘yan jarida a koyaushe a matsayinsu na abokan aiki.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rukunin Farko Na ‘Yan Nijeriya 376 Da Aka Kwaso A Sudan Sun Iso Abuja

Next Post

Hukumar NDE Ta Fara Rajistar Marasa Aiki A Sakkwato

Related

Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

8 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

8 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

9 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

9 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

12 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

13 hours ago
Next Post
Hukumar NDE Ta Fara Rajistar Marasa Aiki A Sakkwato

Hukumar NDE Ta Fara Rajistar Marasa Aiki A Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.