• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Yaba Wa ‘Yan Jarida Bisa Yada Ayyukan Hukumar

by yahuzajere
2 years ago
in Labarai
0
NIS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanturolan Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS), a Jihar Ribas, James Sunday, ya yaba wa ‘yan jarida bisa yadda suke yada ayyukan da hukumar take gudanarwa a cikin kasa da waje.

Kwanturolan wanda ya kasance tsohon jami’in hulda da jama’a na hukumar ya ce a matsayin ‘yan jarida na abokan aiki tare da kawo ci gaba, wajibi ne ya taya su murnar bikin ranarsu wanda aka yi na bana a ranar Laraba 3 ga watan Mayun 2023.

  • Rukunin Farko Na ‘Yan Nijeriya 376 Da Aka Kwaso A Sudan Sun Iso Abuja

Sanarwar da ta fito daga ofishin NIS na Jihar Ribas, ta ce Sunday James ya kuma yi jinjina a kan yadda ‘yan jarida ke wayar da kan jama’a domin su fahimci hakkokinsu na kasa da kuma gudunmawar da ya kamata su bayar wajen gina kasa.

Ya kara da cewa, hukumar ta NIS a Jihar Ribas ta samu kwarin gwiwa wajen bayar da rahoton nasarorin da take samu tare da inganta ayyukanta da take gudanarwa domin ‘yan kasa.

Kwanturolan ya kuma yi amfani da wannan dama ta bikin ranar ‘yan jaridan wajen yaba wa Kwanturola Janar na NIS, Isa Jere Idris, MFR, saboda mutuntawa da hakurin da yake da shi da girmama ‘yancin ‘yan jarida da kuma jajircewarsa na yin aiki tare da kafafen yada labarai a matsayin abokan hadin gwiwa na kawo ci gaba.

Labarai Masu Nasaba

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Ya ba da misalin cewa, kasancewar Kwanturola Janar Jere, ya yi karatunsa na jami’a ne a fannin nazarin sadarwa, hakan ya kara kyautata alakarsa da ‘yan jarida wanda suke samun hadin kansa a duk lokacin da suka zo neman bayani ko Karin haske game da ayyukan da NIS take gudanarwa tun daga lokacin da ya kama aiki a matsayin shugaban hukumar.

Kwanturola James, ya ce ‘yan jarida na da kyakkyawar alaka, hadin gwiwa, da ‘yanci wajen samun bayanan da za su bukata ba tare da kawo cikas ga tsaron kasa daga NIS ba.

Ya kuma hori ‘yan jarida da su kasance masu adalci da kuma da’a ga aikinsu yayin da suke farauto labarai ko tattaunawa da jama’a domin ilmantar da ‘yan kasa. Kana ya hore su a koyaushe su yi kokarin inganta aikinsu tare da kawo sabon salo irin na ci gaban zamani, kana ya ba ta tabbacin NIS za ta ci gaba da kyautata alaka da ‘yan jarida a koyaushe a matsayinsu na abokan aiki.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rukunin Farko Na ‘Yan Nijeriya 376 Da Aka Kwaso A Sudan Sun Iso Abuja

Next Post

Hukumar NDE Ta Fara Rajistar Marasa Aiki A Sakkwato

Related

An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

48 minutes ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

2 hours ago
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai
Labarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

3 hours ago
Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89
Labarai

Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

3 hours ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

5 hours ago
Ministan Tsaro
Labarai

Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya

7 hours ago
Next Post
Hukumar NDE Ta Fara Rajistar Marasa Aiki A Sakkwato

Hukumar NDE Ta Fara Rajistar Marasa Aiki A Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

June 6, 2025
Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

June 6, 2025
Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

June 6, 2025
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

June 6, 2025
aure

Kar Ki Bari Naman Sallah Ya Kashe Miki Aure Yar’uwa

June 6, 2025
Ministan Tsaro

Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.