• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Yaba Wa ‘Yan Jarida Bisa Yada Ayyukan Hukumar

by yahuzajere
2 years ago
in Labarai
0
NIS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanturolan Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS), a Jihar Ribas, James Sunday, ya yaba wa ‘yan jarida bisa yadda suke yada ayyukan da hukumar take gudanarwa a cikin kasa da waje.

Kwanturolan wanda ya kasance tsohon jami’in hulda da jama’a na hukumar ya ce a matsayin ‘yan jarida na abokan aiki tare da kawo ci gaba, wajibi ne ya taya su murnar bikin ranarsu wanda aka yi na bana a ranar Laraba 3 ga watan Mayun 2023.

  • Rukunin Farko Na ‘Yan Nijeriya 376 Da Aka Kwaso A Sudan Sun Iso Abuja

Sanarwar da ta fito daga ofishin NIS na Jihar Ribas, ta ce Sunday James ya kuma yi jinjina a kan yadda ‘yan jarida ke wayar da kan jama’a domin su fahimci hakkokinsu na kasa da kuma gudunmawar da ya kamata su bayar wajen gina kasa.

Ya kara da cewa, hukumar ta NIS a Jihar Ribas ta samu kwarin gwiwa wajen bayar da rahoton nasarorin da take samu tare da inganta ayyukanta da take gudanarwa domin ‘yan kasa.

Kwanturolan ya kuma yi amfani da wannan dama ta bikin ranar ‘yan jaridan wajen yaba wa Kwanturola Janar na NIS, Isa Jere Idris, MFR, saboda mutuntawa da hakurin da yake da shi da girmama ‘yancin ‘yan jarida da kuma jajircewarsa na yin aiki tare da kafafen yada labarai a matsayin abokan hadin gwiwa na kawo ci gaba.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Ya ba da misalin cewa, kasancewar Kwanturola Janar Jere, ya yi karatunsa na jami’a ne a fannin nazarin sadarwa, hakan ya kara kyautata alakarsa da ‘yan jarida wanda suke samun hadin kansa a duk lokacin da suka zo neman bayani ko Karin haske game da ayyukan da NIS take gudanarwa tun daga lokacin da ya kama aiki a matsayin shugaban hukumar.

Kwanturola James, ya ce ‘yan jarida na da kyakkyawar alaka, hadin gwiwa, da ‘yanci wajen samun bayanan da za su bukata ba tare da kawo cikas ga tsaron kasa daga NIS ba.

Ya kuma hori ‘yan jarida da su kasance masu adalci da kuma da’a ga aikinsu yayin da suke farauto labarai ko tattaunawa da jama’a domin ilmantar da ‘yan kasa. Kana ya hore su a koyaushe su yi kokarin inganta aikinsu tare da kawo sabon salo irin na ci gaban zamani, kana ya ba ta tabbacin NIS za ta ci gaba da kyautata alaka da ‘yan jarida a koyaushe a matsayinsu na abokan aiki.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rukunin Farko Na ‘Yan Nijeriya 376 Da Aka Kwaso A Sudan Sun Iso Abuja

Next Post

Hukumar NDE Ta Fara Rajistar Marasa Aiki A Sakkwato

Related

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

12 minutes ago
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

3 hours ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

14 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

20 hours ago
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

21 hours ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

22 hours ago
Next Post
Hukumar NDE Ta Fara Rajistar Marasa Aiki A Sakkwato

Hukumar NDE Ta Fara Rajistar Marasa Aiki A Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

August 24, 2025
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.