• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwastam Za Ta Haɗa Gwiwa Da Al’ummomin Kan Iyakoki Wajen Daƙile Yaɗuwar Makamai

by El-Zaharadeen Umar
1 year ago
Kwastam

Hukumar hana fasa kwauri ta ƙasa, za ta fara yunkuri ta hanyar tattaunawa da al’ummomi da sauran jami’an tsaro domin hana shigowa da makamai Nijeriya. 

Mataimakin shugaban hukumar na ƙasa mai kula da shiyya ta 2 da ke Kaduna, Sambo Dangaladima ne, ya bayyana haka a lokacin wata ziyarar aiki da ya kai a Jihar Katsina.

  • Yarjejeniyar Samoa: Gwamnatin Tarayya Ta Yaba Da Hukuncin NMCC Kan Zargin Auren Jinsi
  • An Gudanar Da Taro Mai Taken “A Rubuce A Sama: Labarina Na Kasar Sin” Don Murnar Cika Shekaru 75 Da Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Kasar Sin a Mexico da Australiya

Ya ƙara da cewa ɗaukar irin wannan mataki ya zama wajibi sakamakon yadda makamai suka yawaita a hannun jama’a.

A cewarsa, hukumar ta shirya ƙara ɗaukar sabbin matakai tare da tsaurara tsaro a kan iyakoki.

Ya ƙara da cewa, za su riƙa yin zama da al’ummomin da ke zaune a kan iyakokin Nijeriya da shugabannin gargajiya domin tattaunawa da ƙara dankon zumunci.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

Da ya juya kan batun jin dadi da walwalar ma’aikatan hukumar, Dangaladima ya jaddada kudirin shugaban hukumar na ƙasa, Bashir Adeniyi na ƙara inganta jin dadi da walwalarsu.

“Tsarin da shugaban hukumar kwastam ya zo da shi, za a duba halin da ma’aikata ke ciki duk da cewar akwai matsalar tattalin arziki.

“Amma duk da haka, za mu ƙara inganta jin dadi da walwalar jami’anmu, inda yanzu haka shirin ya yi nisa” in ji shi.”

Dangaladima ya yi kira ga ma’aikatansu, musamman waɗanda ke kan iyakoki da su ƙara ƙoƙari domin samun nasarar hukumar baƙi ɗaya.

Tunda farko a jawabinsa na maraba, shugaban hukumar a Jihar Katsina, Abba Aji ya bayyana cewa an buɗe kan iyakar Jibia domin fara halastaccen kasuwanci.

Aji ya ƙara da cewa ziyarar da shugaban hukumar na ƙasa mai kula da shiyya ta 2 da ke Kaduna ya kai za ta ƙara taimakawa wajen fadakar da al’umma irin gudunmawar da za su bayar wajen samun nasarar hukumar baƙi ɗaya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140
Labarai

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Majalisar Dattawa
Labarai

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa
Labarai

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Next Post
Tinubu Ya Umarci Ma’aikatu Su Sayi Motoci Masu Amfani Da Gas

Fadar Shugaban Kasa Ta Tabbatar Za A Yi Sauye-sauye A Gwamnatin Tinubu 

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.