ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yarjejeniyar Samoa: Gwamnatin Tarayya Ta Yaba Da Hukuncin NMCC Kan Zargin Auren Jinsi

by Sulaiman
2 years ago
Amurka

Gwamnatin Tarayya ta yaba wa Hukumar Yaƙi Da Ƙorafe-ƙorafen Yaɗa Labarai ta Ƙasa (National Media Complaints Commission, NMCC), mai kula da harkokin yaɗa labarai a Nijeriya, kan hukuncin da ta yanke a kan wata jarida dangane da rahoton bogi da ta buga dangane da yarjejeniyar Samoa.

 

a wata sanarwa da Rabi’u Ibrahim, Mataimaki na Musamman ga Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayar, gwamnatin ta ce, hukuncin ya nuna muhimmancin tabbatar da gaskiya da riƙon amana, tare da tunatar da ‘yan jarida irin muhimmiyar rawar da suke takawa wajen yin tasiri kan fahimtar jama’a ta hanyar bayar da rahotanni na gaskiya.

ADVERTISEMENT
  • Hadimin Tinubu Ya Raba Kayayyakin Makaranta Ga Daliban Firamare A Kano
  • Zargin Ta’addanci A Zamfara: Matawalle Ya Ƙalubalanci Gwamna Dauda Su Yi Rantsuwa Da Alƙur’ani

Haka kuma, ta jaddada cewa dole ne kafafen yaɗa labarai su bi ƙa’idojin aiki don guje wa rahotanni masu cutarwa.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Da take amincewa da ‘yan jarida a matsayin ginshiƙan dimokuraɗiyya, gwamnatin ta yi nuni da cewa, ‘yancin ‘yan jarida yana tafiya ne tare da alhakin bayar da rahotannin gaskiya.

 

Ta kuma yaba da shawarar NMCC ta cewa, tilas ne jaridar ta bai wa jama’a haƙuri tare da kuma ɗaukar matakan hana faruwar irin wannan lamarin a nan gaba.

 

Ta ce: “An yi la’akari da kiran da aka yi ga hukumomin Gwamnatin Tarayya da su ƙara fayyace gaskiya, kuma za a ɗauki matakai don ganin an sanar da ‘yan Nijeriya isassun abubuwan da suka shafi jama’a.”

 

Ta ƙara da cewa, “Gwamnatin Tarayya ta himmatu wajen samar da yanayin da kafafen yaɗa labarai ke bunƙasa tare da ci gaba da bin ƙa’idojin ɗa’a na ma’aikatar.

 

“Muna kira ga dukkan kafafen watsa labarai da su ci gaba da kiyaye waɗannan ƙa’idoji kuma su yi aiki tare wajen yaɗa sahihan bayanai, waɗanda ke da muhimmanci ga ‘yan ƙasa.”

 

Gwamnati ta yi fatan wannan hukunci zai zama wani ma’auni na hazaƙar aikin jarida a Nijeriya, da kuma ƙarfafa danƙon zumunci tsakanin kafafen yaɗa labarai da gwamnati, da al’ummar Nijeriya.

Samoa
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Kwastam Za Ta Haɗa Gwiwa Da Al’ummomin Kan Iyakoki Wajen Daƙile Yaɗuwar Makamai

Kwastam Za Ta Haɗa Gwiwa Da Al'ummomin Kan Iyakoki Wajen Daƙile Yaɗuwar Makamai

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.