• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwastam Za Ta Haɗa Gwiwa Da Al’ummomin Kan Iyakoki Wajen Daƙile Yaɗuwar Makamai

by El-Zaharadeen Umar
1 year ago
Kwastam

Hukumar hana fasa kwauri ta ƙasa, za ta fara yunkuri ta hanyar tattaunawa da al’ummomi da sauran jami’an tsaro domin hana shigowa da makamai Nijeriya. 

Mataimakin shugaban hukumar na ƙasa mai kula da shiyya ta 2 da ke Kaduna, Sambo Dangaladima ne, ya bayyana haka a lokacin wata ziyarar aiki da ya kai a Jihar Katsina.

  • Yarjejeniyar Samoa: Gwamnatin Tarayya Ta Yaba Da Hukuncin NMCC Kan Zargin Auren Jinsi
  • An Gudanar Da Taro Mai Taken “A Rubuce A Sama: Labarina Na Kasar Sin” Don Murnar Cika Shekaru 75 Da Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Kasar Sin a Mexico da Australiya

Ya ƙara da cewa ɗaukar irin wannan mataki ya zama wajibi sakamakon yadda makamai suka yawaita a hannun jama’a.

A cewarsa, hukumar ta shirya ƙara ɗaukar sabbin matakai tare da tsaurara tsaro a kan iyakoki.

Ya ƙara da cewa, za su riƙa yin zama da al’ummomin da ke zaune a kan iyakokin Nijeriya da shugabannin gargajiya domin tattaunawa da ƙara dankon zumunci.

LABARAI MASU NASABA

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

An Kama Wani Mutum Kan Zargin Kashe Matarsa A Sakkwato

Da ya juya kan batun jin dadi da walwalar ma’aikatan hukumar, Dangaladima ya jaddada kudirin shugaban hukumar na ƙasa, Bashir Adeniyi na ƙara inganta jin dadi da walwalarsu.

“Tsarin da shugaban hukumar kwastam ya zo da shi, za a duba halin da ma’aikata ke ciki duk da cewar akwai matsalar tattalin arziki.

“Amma duk da haka, za mu ƙara inganta jin dadi da walwalar jami’anmu, inda yanzu haka shirin ya yi nisa” in ji shi.”

Dangaladima ya yi kira ga ma’aikatansu, musamman waɗanda ke kan iyakoki da su ƙara ƙoƙari domin samun nasarar hukumar baƙi ɗaya.

Tunda farko a jawabinsa na maraba, shugaban hukumar a Jihar Katsina, Abba Aji ya bayyana cewa an buɗe kan iyakar Jibia domin fara halastaccen kasuwanci.

Aji ya ƙara da cewa ziyarar da shugaban hukumar na ƙasa mai kula da shiyya ta 2 da ke Kaduna ya kai za ta ƙara taimakawa wajen fadakar da al’umma irin gudunmawar da za su bayar wajen samun nasarar hukumar baƙi ɗaya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama
Manyan Labarai

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato
Labarai

An Kama Wani Mutum Kan Zargin Kashe Matarsa A Sakkwato

November 6, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa
Labarai

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Don Karɓo Rancen N1.15trn Don Cike Giɓin Kasafin Kuɗin 2025

November 6, 2025
Next Post
Tinubu Ya Umarci Ma’aikatu Su Sayi Motoci Masu Amfani Da Gas

Fadar Shugaban Kasa Ta Tabbatar Za A Yi Sauye-sauye A Gwamnatin Tinubu 

LABARAI MASU NASABA

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

An Kama Wani Mutum Kan Zargin Kashe Matarsa A Sakkwato

November 6, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Don Karɓo Rancen N1.15trn Don Cike Giɓin Kasafin Kuɗin 2025

November 6, 2025
Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

November 6, 2025
Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

November 6, 2025
Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

November 6, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro

November 6, 2025
Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.