ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kyakkyawar Alakar Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka Na Haifar Da Ci Gaba Mai Armashi

by CMG Hausa
2 years ago
Afirka

Bayan kammalar taron kolin BRICS na kwanakin baya, masharhanta na ta tofa albarkacin bakinsu, game da tasirin kyakkyawan yanayin hadin gwiwar Sin da nahiyar Afirka, musamman ta la’akari da kalaman da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya furta, yayin taron tattaunawa a tsakanin shugabannin Sin da na Afirka a birnin Johannesburg na Afirka ta Kudu.

A cikin kalaman shugaba Xi, ya bayyana bukatar dake akwai ta Sin da Afirka su yi hadin gwiwa, wajen sa kaimi ga tabbatar da odar kasa da kasa bisa adalci, da kiyaye yanayin duniya mai zaman lafiya da tsaro, da kuma raya tattalin arzikin duniya mai bude kofa ga kowa.

  • Zaɓin Hanyar Ci Gaba Tare Ta BRICS Ya Ja Hankalin Duniya

Ko shakka babu, akasarin masu sharhi sun gamsu da manufar kasar Sin, ta “A Gudu Tare A Tsira Tare”, inda suke kafa misali da yadda hadin gwiwar sassan biyu ya samar da wani ginshiki, na gina muhimman ababen more rayuwa masu ingiza ci gaban tattalin arziki da zamantakewar al’ummar nahiyar Afirka, matakin dake taimakawa matuka ga bunkasa masana’antu, da kyautata hada-hadar cinikayya a kasashen Afirka.

ADVERTISEMENT

A zahiri take cewa, a baya bayan nan, kasar Sin ta wuce gaba a fannin yin hadin gwiwa da kasashen Afirka, inda ba ya ga batun tattalin arziki da cinikayya, Sin din na daukar kasashen nahiyar Afirka a matsayin abokan gina makoma, wadda ’yan baya za su ci gajiyarta.

Wasu daga masharhanta ma na ganin yayin da alakar Sin da Afirka ke kara zurfafa, nan gaba sassan biyu za su karkata ga kulla hadin gwiwar raya fannin manyan fasahohi, irinsu kwaikwayon tunanin bil adama, da binciken sararin samaniya, da sauran muhimman sassa da duniya ke mayar da hankali yanzu a kansu.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

Fatan da dukkanin sassan nahiyar Afirka ke yi a halin yanzu, shi ne dorewar kyakkyawar dangantaka mai armashi tsakaninsu da kasar Sin, ta yadda za su ci gaba da cin gajiya, da bunkasa kawancen gargajiya mai dadadden tarihi tsakaninsu da Sin. (Saminu Alhassan)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025
Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

November 12, 2025
Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa
Daga Birnin Sin

Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

November 12, 2025
Next Post
Gwamnan Zamfara Ya Yi Alkawarin Ci Gaba Da Yakar ‘Yan Bindiga

Gwamnan Zamfara Ya Yi Alkawarin Ci Gaba Da Yakar 'Yan Bindiga

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Wasan Ƙwallon Ƙafa 10 Da Za Su Iya Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ta Ƙarshe A 2026

‘Yan Wasan Ƙwallon Ƙafa 10 Da Za Su Iya Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ta Ƙarshe A 2026

November 13, 2025
Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

November 13, 2025
Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

November 13, 2025
Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

November 13, 2025
Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025
Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 12, 2025
Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

November 12, 2025
Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

November 12, 2025
'yansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.