• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kyakkyawar Alakar Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka Na Haifar Da Ci Gaba Mai Armashi

by CMG Hausa
2 years ago
Afirka

Bayan kammalar taron kolin BRICS na kwanakin baya, masharhanta na ta tofa albarkacin bakinsu, game da tasirin kyakkyawan yanayin hadin gwiwar Sin da nahiyar Afirka, musamman ta la’akari da kalaman da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya furta, yayin taron tattaunawa a tsakanin shugabannin Sin da na Afirka a birnin Johannesburg na Afirka ta Kudu.

A cikin kalaman shugaba Xi, ya bayyana bukatar dake akwai ta Sin da Afirka su yi hadin gwiwa, wajen sa kaimi ga tabbatar da odar kasa da kasa bisa adalci, da kiyaye yanayin duniya mai zaman lafiya da tsaro, da kuma raya tattalin arzikin duniya mai bude kofa ga kowa.

  • Zaɓin Hanyar Ci Gaba Tare Ta BRICS Ya Ja Hankalin Duniya

Ko shakka babu, akasarin masu sharhi sun gamsu da manufar kasar Sin, ta “A Gudu Tare A Tsira Tare”, inda suke kafa misali da yadda hadin gwiwar sassan biyu ya samar da wani ginshiki, na gina muhimman ababen more rayuwa masu ingiza ci gaban tattalin arziki da zamantakewar al’ummar nahiyar Afirka, matakin dake taimakawa matuka ga bunkasa masana’antu, da kyautata hada-hadar cinikayya a kasashen Afirka.

A zahiri take cewa, a baya bayan nan, kasar Sin ta wuce gaba a fannin yin hadin gwiwa da kasashen Afirka, inda ba ya ga batun tattalin arziki da cinikayya, Sin din na daukar kasashen nahiyar Afirka a matsayin abokan gina makoma, wadda ’yan baya za su ci gajiyarta.

Wasu daga masharhanta ma na ganin yayin da alakar Sin da Afirka ke kara zurfafa, nan gaba sassan biyu za su karkata ga kulla hadin gwiwar raya fannin manyan fasahohi, irinsu kwaikwayon tunanin bil adama, da binciken sararin samaniya, da sauran muhimman sassa da duniya ke mayar da hankali yanzu a kansu.

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

Fatan da dukkanin sassan nahiyar Afirka ke yi a halin yanzu, shi ne dorewar kyakkyawar dangantaka mai armashi tsakaninsu da kasar Sin, ta yadda za su ci gaba da cin gajiya, da bunkasa kawancen gargajiya mai dadadden tarihi tsakaninsu da Sin. (Saminu Alhassan)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik
Daga Birnin Sin

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

October 29, 2025
Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki
Daga Birnin Sin

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

October 29, 2025
An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest
Daga Birnin Sin

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

October 29, 2025
Next Post
Gwamnan Zamfara Ya Yi Alkawarin Ci Gaba Da Yakar ‘Yan Bindiga

Gwamnan Zamfara Ya Yi Alkawarin Ci Gaba Da Yakar 'Yan Bindiga

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

October 30, 2025
Afirka

Bai Kamata Gwamnati Ta Ke Ciyo Bashi Bayan Cire Tallafin Man Fetur Ba – Sanusi II

October 30, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Sauya Sunayen Waɗanda Aka Yi Wa Afuwa

October 30, 2025
Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

October 29, 2025
Asuu

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025
Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

October 29, 2025
Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

October 29, 2025
An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

October 29, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya

October 29, 2025
An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

October 29, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.