• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kyautata Alakar Sin Da Amurka Na Iya Shawo Kan Matsalolin Duniya

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kyautata Alakar Sin Da Amurka Na Iya Shawo Kan Matsalolin Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da taron koli na kungiyar G20 zai mayar da hankali wajen tattauna muhimman batutuwan da ke ciwa duniya tuwo a kwarya, kamar na tattalin arziki da wadatar abinci da makamashi da batun Ukraine da sauransu, ya samar da wata muhimmiyar dama ta tattaunawar keke da keke, tsakanin shugabannin manyan kasashen duniya biyu, wato Sin da Amurka.

Karon farko tun bayan hawansa karagar mulkin Amurka, shugaba Joe Biden ya gana ido da ido da takwaransa na kasar Sin Xi Jinping a jiya, gabanin taron.

  • Xi Jinping: Sin Na Goyon Bayan Shigar Da Kungiyar AU G20

Hakika, wannan wata dama ce ta warware zare da abawa game da batutuwan dake haifar da tsamin dangantaka tsakanin manyan kasashen biyu.

Amurka ta dade tana takalar kasar Sin da gangan, yayin da a kullum, kasar Sin kan gargadi Amurkar tare da jan hankalinta game da muhimmancin girmama juna da hadin gwiwa a tsakaninsu.

Da alama za a samu saukin abubuwa, duba da yadda shugaban na Amurka ya nanata cewa, matsayar kasarsa ta kiyaye manufar Sin daya tak a duniya ba ta sauya ba, kuma ba ta son gogayya tsakaninsu ta rikide zuwa rikici. Gogayya ko Takara mai tsafta tsakanin manyan kasashen biyu mai, za ta iya zama mai amfanawa al’ummunsu da kuma duniya, muddun Amurka ba ta ci gaba da yin amai tana lashewa ba.

Labarai Masu Nasaba

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Kamata ya yi ta dauki shawarar kasar Sin, wato mutunta juna da girma cikakken ’yanci da moriyar juna, su kasance tushen huldar kasashen biyu. Kana akwai bukatar ’yan siyasar Amurka, su fahimta tare da kiyaye furucin na shugabansu, su dakatar da duk wani yunkurin lalata dangantaka a tsakanin kasashen biyu da neman haddasa rigima.

Kamar yadda shugaba Xi Jinping ya bayyana, a matsayinsu na shugabannin manyan kasashe biyu, ya kamata su lalubo hanyar da ta dace da kyautata dangantakarsu, domin yanayin da take ciki a yanzu, ba ta dace da moriyarsu da ma ta daukacin al’ummar duniya ba.

Ba shakka, kasashen duniya na mayar da hankalinsu ga irin yanayin da Sin da Amurka ke ciki. Kyautata alaka a tsakaninsu za ta iya magance sama da rabin batutuwan da duniya ke fuskanta.

Haka kuma, za ta kasance abun koyi ga kasashe masu tasowa. Ya kamata Amurka ta mara baya ga yunkurin Sin na tallafawa kasashe masu rauni da ma wadanda ke tasowa, maimakon ta rika yi mata zagon kasa ko neman bata mata suna. Sin ta yi an gani, kuma tana ci gaba da taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da zaman lafiya da ci gaba a duniya duk da tarin nauyin al’umma biliyan 1.4 dake wuyanta a cikin gida. Idan har da gaske Amurka na son kyautata dangantakarsu domin duniya baki daya ta amfana, ya kamata ta dakatar da rajinta na bata sunan kasar Sin da yada karairayi, ta rungumi hanyar zaman lafiya da bayar da gudunmawa ga kokarin Sin domin kai wa ga gina al’umma mai kyakkyawar makoma ga daukacin bil adama. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojoji Sun Kashe Shugabannin ‘Yan Bindiga Buzu, Ganai Da sauransu A Harin Jirgin Yaki

Next Post

A Dauki Hakikakin Matakai Domin Kyautata Hulda A Tsakanin Sin Da Amurka

Related

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?
Daga Birnin Sin

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

11 hours ago
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

12 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

14 hours ago
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

14 hours ago
Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya
Daga Birnin Sin

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

16 hours ago
Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC
Daga Birnin Sin

Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC

17 hours ago
Next Post
Sin

A Dauki Hakikakin Matakai Domin Kyautata Hulda A Tsakanin Sin Da Amurka

LABARAI MASU NASABA

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

August 27, 2025
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

August 27, 2025
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

August 27, 2025
Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hukumar NRC Ta Dakatar Da Zirga-zirgar Jiragen Kasa Na Abuja zuwa Kaduna

August 26, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

August 26, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.