• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kyautata Alakar Sin Da Amurka Na Iya Shawo Kan Matsalolin Duniya

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kyautata Alakar Sin Da Amurka Na Iya Shawo Kan Matsalolin Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da taron koli na kungiyar G20 zai mayar da hankali wajen tattauna muhimman batutuwan da ke ciwa duniya tuwo a kwarya, kamar na tattalin arziki da wadatar abinci da makamashi da batun Ukraine da sauransu, ya samar da wata muhimmiyar dama ta tattaunawar keke da keke, tsakanin shugabannin manyan kasashen duniya biyu, wato Sin da Amurka.

Karon farko tun bayan hawansa karagar mulkin Amurka, shugaba Joe Biden ya gana ido da ido da takwaransa na kasar Sin Xi Jinping a jiya, gabanin taron.

  • Xi Jinping: Sin Na Goyon Bayan Shigar Da Kungiyar AU G20

Hakika, wannan wata dama ce ta warware zare da abawa game da batutuwan dake haifar da tsamin dangantaka tsakanin manyan kasashen biyu.

Amurka ta dade tana takalar kasar Sin da gangan, yayin da a kullum, kasar Sin kan gargadi Amurkar tare da jan hankalinta game da muhimmancin girmama juna da hadin gwiwa a tsakaninsu.

Da alama za a samu saukin abubuwa, duba da yadda shugaban na Amurka ya nanata cewa, matsayar kasarsa ta kiyaye manufar Sin daya tak a duniya ba ta sauya ba, kuma ba ta son gogayya tsakaninsu ta rikide zuwa rikici. Gogayya ko Takara mai tsafta tsakanin manyan kasashen biyu mai, za ta iya zama mai amfanawa al’ummunsu da kuma duniya, muddun Amurka ba ta ci gaba da yin amai tana lashewa ba.

Labarai Masu Nasaba

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Kamata ya yi ta dauki shawarar kasar Sin, wato mutunta juna da girma cikakken ’yanci da moriyar juna, su kasance tushen huldar kasashen biyu. Kana akwai bukatar ’yan siyasar Amurka, su fahimta tare da kiyaye furucin na shugabansu, su dakatar da duk wani yunkurin lalata dangantaka a tsakanin kasashen biyu da neman haddasa rigima.

Kamar yadda shugaba Xi Jinping ya bayyana, a matsayinsu na shugabannin manyan kasashe biyu, ya kamata su lalubo hanyar da ta dace da kyautata dangantakarsu, domin yanayin da take ciki a yanzu, ba ta dace da moriyarsu da ma ta daukacin al’ummar duniya ba.

Ba shakka, kasashen duniya na mayar da hankalinsu ga irin yanayin da Sin da Amurka ke ciki. Kyautata alaka a tsakaninsu za ta iya magance sama da rabin batutuwan da duniya ke fuskanta.

Haka kuma, za ta kasance abun koyi ga kasashe masu tasowa. Ya kamata Amurka ta mara baya ga yunkurin Sin na tallafawa kasashe masu rauni da ma wadanda ke tasowa, maimakon ta rika yi mata zagon kasa ko neman bata mata suna. Sin ta yi an gani, kuma tana ci gaba da taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da zaman lafiya da ci gaba a duniya duk da tarin nauyin al’umma biliyan 1.4 dake wuyanta a cikin gida. Idan har da gaske Amurka na son kyautata dangantakarsu domin duniya baki daya ta amfana, ya kamata ta dakatar da rajinta na bata sunan kasar Sin da yada karairayi, ta rungumi hanyar zaman lafiya da bayar da gudunmawa ga kokarin Sin domin kai wa ga gina al’umma mai kyakkyawar makoma ga daukacin bil adama. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojoji Sun Kashe Shugabannin ‘Yan Bindiga Buzu, Ganai Da sauransu A Harin Jirgin Yaki

Next Post

A Dauki Hakikakin Matakai Domin Kyautata Hulda A Tsakanin Sin Da Amurka

Related

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

12 minutes ago
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

1 hour ago
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata
Daga Birnin Sin

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

2 hours ago
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”
Daga Birnin Sin

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

3 hours ago
Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin

5 hours ago
An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

21 hours ago
Next Post
Sin

A Dauki Hakikakin Matakai Domin Kyautata Hulda A Tsakanin Sin Da Amurka

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
Sin

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin

Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin

September 19, 2025
An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

September 19, 2025
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.