• English
  • Business News
Tuesday, July 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping: Sin Na Goyon Bayan Shigar Da Kungiyar AU G20

by Sulaiman and CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Xi Jinping: Sin Na Goyon Bayan Shigar Da Kungiyar AU G20
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da safiyar yau Talata ne aka bude zaman farko na taron kolin G20, a tsibirin Bali na kasar Indonesiya, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya halarci taron, ya kuma gabatar da jawabi.

A jawabin nasa Xi Jinping ya ce, a halin yanzu, ana fuskantar babban kalubalen raya kasashen duniya. Don haka ya kamata mambobin G20 su sauke nauyin dake bisa wuyansu a matsayinsu na manyan kasashen duniya, domin neman bunkasuwar kasa da kasa, da tallafawa alummun duniya, yayin da ake tabbatar da ci gaban duniya baki daya.

Ya kuma kara da cewa, a halin yanzu, kasashen duniya, musamman ma kasashe masu tasowa suna fuskantar kalubalen raguwar tattalin arziki.

Don haka ya ba da shawarar kafa dangantakar abokantaka ta neman farfado da tattalin arzikin duniya, da mai da aikin neman ci gaba, da raya alumma a matsayin babban aikin da aka sanya gaba, tare da mai da hankali kan bukatun kasashe maso tasowa. Kaza lika ya ce kasar Sin tana goyon bayan shigar da kungiyar tarayyar kasashen Afirka wato AU kungiyar G20.

Haka kuma, cikin jawabinsa, shugaba Xi ya bayyana cewa, a halin yanzu, ya kamata a nemi ci gaban da kowace kasa za ta iya cin gajiya.

Labarai Masu Nasaba

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

Ci gaban da kowace kasa za ta ci gajiya tare, hakikanin ci gaba ne da ake bukata. Ya kamata kasashen dake kan gaba wajen samun ci gaba, su ba da taimako yadda ya kamata ga sauran kasashe, da kuma samar musu karin damammakin da suke bukata.

Ya ce, Kalubaloli masu tsanani da ake fuskanta wajen neman bunkasuwar kasashen duniya, su ne babu isashen hatsi da makamashi. Kuma, muhimmiyar hanyar da za mu yi amfani da ita wajen shawo kan wadannan kalubaloli ita ce, yin hadin gwiwa kan aikin sa ido a kasuwanni, da kuma kafa manyan kasuwannin bude kofa ga waje, domin karfafa tsarin samar da kayayyaki cikin hadin gwiwa, da kuma daidaita farashin kayayyaki yadda ya kamata.

Bugu da kari, Xi Jinping ya ce, a yayin babban taron wakilan Jam’iyyar Kwaminis ta Kasar Sin karo na 20 da aka yi watan jiya, an tabbatar da burin ci gaban kasar Sin da na JKS cikin shekaru 5 masu zuwa.

Kuma kasar Sin za ta tsaya tsayin daka wajen neman bunkasuwa cikin lumana, da zurfafa aikin kwaskwarima, da kuma kara bude kofa ga waje, domin neman farfadowar kasar Sin baki daya ta hanyar zamanintar da kasar. (Mai Fassarawa: Maryam Yang)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping: Sin Na Goyon Bayan Shigar Da Kungiyar AU G20

Next Post

Osinbajo Bai Halarci Taron Yakin Neman Zaben APC A Filato Ba

Related

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

8 hours ago
Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

9 hours ago
Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

10 hours ago
Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan
Daga Birnin Sin

Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

10 hours ago
Sin Na Bikin Cika Shekaru 88 Da Dukkan Al’ummar Kasar Ta Fara Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan
Daga Birnin Sin

Sin Na Bikin Cika Shekaru 88 Da Dukkan Al’ummar Kasar Ta Fara Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan

11 hours ago
Firaministan Kasar Sin: Kasarsa Ta Kimtsa Tsaf Wajen Inganta Aikin BRI Da Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Tare Da Habasha
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin: Kasarsa Ta Kimtsa Tsaf Wajen Inganta Aikin BRI Da Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Tare Da Habasha

12 hours ago
Next Post
Osinbajo Bai Halarci Taron Yakin Neman Zaben APC A Filato Ba

Osinbajo Bai Halarci Taron Yakin Neman Zaben APC A Filato Ba

LABARAI MASU NASABA

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

July 8, 2025
Da ÆŠumi-ÆŠumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Da ÆŠumi-ÆŠumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 7, 2025
Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

July 7, 2025
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar HaÉ—aka Ta ADC

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar HaÉ—aka Ta ADC

July 7, 2025
Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

July 7, 2025
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

July 7, 2025
Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

July 7, 2025
Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

July 7, 2025
Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage KuÉ—i Kaso 50%

Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage KuÉ—i Kaso 50%

July 7, 2025
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda ÆŠumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda ÆŠumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

July 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.