• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Labaran Karyar Cewa “Tattalin Arzikin Sin Na Dakushewa” Ba sa Tasiri A zukatan Jama’a 

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Labaran Karyar Cewa “Tattalin Arzikin Sin Na Dakushewa” Ba sa Tasiri A zukatan Jama’a 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A cikin ’yan shekarun da suka gabata, wasu ’yan siyasa, da kafofin watsa labaru, da masana kimiyya na yammacin duniya, sun shirya jerin labaran karya na cewa “tattalin arzikin kasar Sin na dakushewa bayan da ya kai kololuwa,” da nufin dakile hasashen ci gaban kasar Sin. Musamman tun daga rubu’i na biyu na shekarar 2023, kusan dukkanin manyan kafofin watsa labaru na yammacin duniya, da masana da suka fi maida hankali kan kasar Sin, sun shiga cikin jerin masu sukar tattalin arzikin kasar Sin.

Jaridar Wall Street Journal babban misali ce. Inda daga watan Agustan shekarar 2023 zuwa farkon shekarar 2024, ta wallafa labarai sama da 160, ciki har da mai taken “Karshen bunkasar tattalin arzikin kasar Sin na shekaru 40: Mene ne zai biyo baya?” “Tattalin arzikin kasar Sin ya shiga cikin mummunan da’ira,” da dai sauran su.

  • Kakakin Taron Majalisar NPC: Sin Za Ta Ci Gaba Da Kokarin Kare Ikonta Na Mallakar Yankunan Kasa
  • An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Mata Ta Kasa Da Kasa A Beijing

Sun rufe idanunsu ga hujjoji wadanda ke bayyana bunkasuwar tattalin arzikin Sin a zahiri. Ba wai kawai sun yi kokarin kawo tsaiko ga baiwa alkiblar sauye-sauyen tattalin arzikin kasar Sin damar samun bunkasuwa mai inganci ba, har ma sun yi watsi da gaskiyar cewa kasar Sin ce ke kan gaba a duniya wajen samun bunkasuwar tattalin arziki na hakika.

Misali, kayayyakin da kasar Sin take fitarwa da aka yiwa lakabi da “Sabbin Zakaru Uku” wato kayayyakin sassan makamashin hasken rana wanda a halin yanzu kasar Sin ke rike da kashi 50 cikin dari na kasuwarsa a duniya, da motoci masu amfani da sabbin makamashi wanda a bara ta fitar da guda miliyan 1.2 wato karuwar kashi 77.6 cikin dari, da batirin Lithium inda kamfanonin kasar Sin guda shida ke cikin jerin manyan kamfanoni goma na duniya dake samar da shi. Wadannan sabbin zakaru guda uku suna ba da gagaruwar gudummawa wajen rage tasirin sauyin yanayi tare da bunkasa tattalin arziki kasar Sin. Duk da haka masu sukar tattalin arzikin kasar Sin ba su mai da hankali sun sanya wannan gagarumar ci gabar a cikin labaransu na karyar “dakushewar tattalin arzikin Sin” ba.

Bara mu kwatanta muhimman bayanan tattalin arziki tsakanin Sin da Amurka a shekarar da ta gabata, farawa da yawan motocin da kasar Sin ta siyar da ya kai miliyan 30.1 wanda ya ninka na Amurka, Yawan danyen karafa da kasar Sin ta samar ya kai sama da tan biliyan 1.02, ya ninka na Amurka sau 12.6, kuma adadin aikin gina jiragen ruwa da kasar Sin ta kammala ya kai nauyin tan miliyan 42.32 wanda ya ninka na Amurka fiye da sau 70. Wadanna nasarori na nuni da karfi da ci gaban tattalin arzikin Sin.

Labarai Masu Nasaba

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

A karshe, yayin da ake zurfafa yin gyare-gyare a gida da bude kofa ga waje, tattalin arzikin kasar Sin na kara girma, kuma ana ci gaba da samun bunkasuwa da samun moriyar jama’ar kasar Sin da ma duniya baki daya, tabbas labaransu na karyar cewa “Tattalin arzikin Sin na dakushewa” ba sa tasiri a zukatan jama’a.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Sin Za Ta Bude Zamanta Na Shekara A Gobe Talata

Next Post

Shugaba Tinubu Ya Dawo Abuja Daga Qatar

Related

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

10 hours ago
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

11 hours ago
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12
Daga Birnin Sin

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

12 hours ago
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana
Daga Birnin Sin

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

13 hours ago
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

14 hours ago
Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa
Daga Birnin Sin

Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa

15 hours ago
Next Post
Shugaba Tinubu Ya Dawo Abuja Daga Qatar

Shugaba Tinubu Ya Dawo Abuja Daga Qatar

LABARAI MASU NASABA

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

August 23, 2025
Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

August 23, 2025
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

August 23, 2025
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.