• English
  • Business News
Tuesday, October 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 weeks ago
Xinjiang

Abokai, a cikin shirin “Labaran Xinjiang a zane” a yau, za mu duba yanayin fannin ba da ilmi a jihar Xinjiang ta Sin.

A bana, iyalin Maitibake Tuersongmaiti,mazaunin kauyen Tuohula dake gundumar Hotan na Xinjiang, suna cikin farin ciki. “Yarona ya shiga makarantar midil, ya tafi wani wuri mai kyau a fannin muhallin rayuwa don karatu, saboda haka mun yi farin ciki sosai,” in ji Maitibake. Yana da ’ya’ya uku, babban dansa ya shiga makarantar midil ta goma ta birnin Karamay, dansa na biyu yana makarantar firamare a kauyensu, kana karamar cikinsu, ta shiga gidan renon kananan yara a watan Satumban da ya gabata. Ya ce, “Duk ’ya’yana uku suna zuwa makarantu a kusa da gida, kuma suna karatu a kyauta, yayin da yanayin makarantu ya fi na lokacinmu sosai.Malamansu dukkansu sun yi karatun jami’a.”

Sauye-sauyen da aka samu ta fuskar aikin ilimi a kauyen Buzhak na Hotan, misali ne na bunkasuwar aikin ba da ilmin tilas kyauta a Xinjiang.

Shekaru 70 da suka gabata, jami’a daya kacal da makarantun sakandare tara, da makarantun firamare 1,355 kacal jihar Xinjiang ke da su, kuma kashi 19.8% na yaran da suka isa shekarun makaranta ne kawai ke shiga makaranta, kana kashi 90% na mutanen yankin jahilai ne. Amma yanzu, a jihar Xinjiang, akwai makarantar kula da kananan yara daya ga duk yara 106, makarantar firamare daya ga duk yara 817, kuma kashi 97.74% na yaran sun shiga makarantar sakandare.

Yanzu a Xinjiang, mafi kyawun gine-gine su ne makarantu, kuma mafi kyawun wurin shakatawa shi ne harabar makaranta. Ci gaban da ake samu a Xinjiang wajen ba da ilimi yana ta samun ingantuwa, daga matsayin “samun makaranta” zuwa na “samun ingantaccen ilimi.” Bambance-bambancen ingancin aikin ilimi tsakanin yankuna, kauyuka da birane, da makarantu, suna raguwa bisa tallafin gwamnati da amfani da fasahar zamani, da ingantaccen rabon albarkatu. Karin iyalai kamar na Maitibake suna da kyakkyawar damar tabbatar da makoma mai haske, da cimma burikan da suka sanya, ta hanyar neman karin ilimi.(Mai zane da rubutu: MINA)

LABARAI MASU NASABA

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa
Ra'ayi Riga

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

October 21, 2025
Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa
Ra'ayi Riga

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

October 21, 2025
Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang
Ra'ayi Riga

Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

October 13, 2025
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Fara Biyan Ƙarin ₦32,000 Ga ‘Yan Fansho

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Biyan Ƙarin ₦32,000 Ga 'Yan Fansho

LABARAI MASU NASABA

Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Gwamna Yusuf Ya Buƙaci Hukumar NBC Da Ta Sa Ido Kan Gidajen Rediyo Da Talabijin Na Yanar Gizo

October 21, 2025
Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

October 21, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Tabbatar Da Yusuf A Matsayin Sabon Shugaban NPC, Wasu 2 A Matsayin Kwamishinoni

October 21, 2025
Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

October 21, 2025
Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

Ma’aikatan Manyan Makarantu Na Kaduna Sun Dakatar Da Yajin Aiki Yayin Da Gwamna Sani Ya Amince Da Sabon Tsarin Albashi

October 21, 2025
Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

October 21, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Wata Tankar Mai Ta Sake Fashewa A Neja

Da Ɗumi-ɗumi: Fashewar Tankar Man Fetur Ta Yi Ajalin Rayuka 30 A Neja

October 21, 2025
Sin Ta Bayar Da Tallafin Dala Miliyan 3.5 Ga Shirin Samar Da Abinci A Zambia

Sin Ta Bayar Da Tallafin Dala Miliyan 3.5 Ga Shirin Samar Da Abinci A Zambia

October 21, 2025
Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya

Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya

October 21, 2025
An Ɗage Shari’ar Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Zuwa 19 Ga Watan Nuwamba

An Ɗage Shari’ar Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Zuwa 19 Ga Watan Nuwamba

October 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.