Firaministan kasar Sin Li Qiang ya taya Allah-Maye Halina murnar zama sabon firaministan kasar Chadi.
A cikin sakon taya murnar da ya aike masa a jiya, Li Qiang ya bayyana cewa, gwamnatin kasar Sin tana bayar da muhimmanci matuka ga raya dangantakar dake tsakaninta da Chadi. Kuma yana son yin kokari tare da firaminista Halina wajen zurfafa imani da juna a fannin siyasa da fadada hadin gwiwarsu, ta yadda za a inganta dangantakar abokantaka a tsakanin kasashen biyu. (Zainab Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp