• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

by Abubakar Sulaiman
21 seconds ago
in Manyan Labarai
0
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ƙungiyar Likitoci masu neman ƙwarewa (Resident Doctors) a ƙarƙashin Hukumar Kula da Birnin Tarayya (ARD-FCTA) ta sanar da shiga yajin aiki na dindindin bayan ƙarewar yajin aikin gargaɗi na kwana bakwai da suka fara tun 8 ga Satumba, 2025.

Wannan mataki ya fito ne a cikin wata sanarwa da shugabannin ƙungiyar, Dr. George Ebong (Shugaba) da Dr. Agbor Affiong (Sakataren Ƙoli), suka sanya wa hannu a safiyar Litinin.

  • PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya
  • Majalisa Ta Bai Wa Minista Sa’o’i 48 Ya Bayyana A Gabanta Kan Hatsarin Jirgin Abuja Zuwa Kaduna

Ƙungiyar ta bayyana Ƙorafe-ƙorafen da suka shafi biyan bashin albashi tsakanin wata 1 zuwa 6 ga likitocin da aka ɗauka tun 2023, rashin biyan kuɗin atisaye (Medical Residency Training Fund (MRTF)) na 2025, jinkirin ƙarin matsayi, da ci gaba da rage musu albashi ba bisa ƙa’ida ba.

Haka kuma, sun koka da rashin ɗaukar sabbin likitoci duk da ƙarancin ma’aikata a asibitocin FCT, abin da suka ce ya haddasa mutuwar wasu ma’aikatan lafiya saboda gajiya da damuwa, tare da jefa lafiyar marasa lafiya da likitoci cikin “babban haɗari mai iya zama bala’i.”

ARD-FCTA ta jaddada buƙatunta da suka haɗa da biyan dukkan bashin albashi, da ɗaukar sabbin likitoci kafin ƙarshen 2025, biyan cikakken alawus na MRTF, da kuma gyaran asibitocin FCT cikin gaggawa. Sun kuma bukaci a ayyana dokar ta baci a asibitocin FCT, inda suka ce babban birnin ƙasar da ya kamata ya zama abin koyi a kiwon lafiya ya koma “ƙasa da matsayin da ya dace da shi.”

Labarai Masu Nasaba

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbujaAsibitiLikitoci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Related

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano
Manyan Labarai

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

2 hours ago
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba
Manyan Labarai

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

15 hours ago
Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?
Manyan Labarai

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

19 hours ago
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

23 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

1 day ago
Likitoci
Manyan Labarai

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

1 day ago

LABARAI MASU NASABA

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

September 15, 2025
Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

September 15, 2025
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

September 15, 2025
Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

September 15, 2025
Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

September 15, 2025
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

September 14, 2025
An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

September 14, 2025
Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

September 14, 2025
Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.