• English
  • Business News
Monday, June 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Likitocin Sin Masu Aikin Jinya A Afirka Sun Zamo Jakadun Wanzar Da Kawance

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Likitocin Sin Masu Aikin Jinya A Afirka Sun Zamo Jakadun Wanzar Da Kawance
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A bana ne ake cika shekaru 60 tun bayan da kasar Sin ta fara aikewa da jami’an kiwon lafiya masu aikin jin kai zuwa kasashen Afirka daban daban. A sassa da dama a nahiyar Afirka, tawagogin likitocin na Sin sun yi rawar gani, wajen taimakawa mazauna wuraren, har ta kai ana kiran su da “Wakilai na gari kuma jakadun wanzar da kawance”, matsayin da ko shakka babu ya dace da godiyar da al’ummun nahiyar ke yiwa wadannan jami’ai masu aikin sadaukar da kai.

Tun bayan aikewa da tawagar irin wadannan likitoci na Sin zuwa kasar Aljeriya a watan Afrilun shekarar 1963, Sin ta ci gaba da aikewa da tawagogi daban daban zuwa Afirka. Baya ga kayan aiki da horaswa a fannin sanin makamar aiki da tawagogin ke samarwa a nahiyar.

  • Xi Ya Yi Kira Da A Nace Ga Alakar Sin Da Faransa Bisa Manyan Tsare-Tsare

Cikin sama da shekarun nan 60, Sin ta aike da tawagogin tallafin jinya mai kunshe da jimillar mambobi 30,000 zuwa kasashe da yankunan duniya 76, a sassan nahiyoyin duniya 5. Wasu alkaluman sun nuna cewa, adadin marasa lafiya da rukunonin likitocin Sin masu aikin jin kai suka yiwa jinya ya kai miliyan 290. Kaza lika a yanzu haka, wasu tawagogin likitocin na Sin na aiki a wurare 115 dake kasashe 57, kuma kusan rabin su na aiki ne a wurare masu wuyar kaiwa da yanayi mai tsanani.

Sanin kowa ne cewa nahiyar Afirka na shan fama da cututtuka masu yaduwa, kamar zazzabin cizon sauro ko Malaria, da Amai da gudanawa, da zazzabin shawara da sauran su, cututtukan da masana ke cewa karancin ababen more rayuwa ta fuskar kiwon lafiya, da kwararrun jami’an lafiya ne ke kara ta’azzara yaduwar su. Don haka ne ma rukunonin likitocin da Sin ke turawa suka dukufa, wajen samar da jinya ga dubun dubatar al’ummun nahiyar masu bukatar taimako.

Ko shakka babu rukunonin likitocin Sin sun cancanci yabo, bisa yadda suka gudanar da aikin tiyatar zuciya irin sa na farko a kasar Sudan, da dashen na’urar taimakawa zuciya irin sa na farko a Gambia, da aikin kwakwalwa irin sa na farko a kasar Benin, da dashen kafada a Mozambique da dai sauran su.

Labarai Masu Nasaba

Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin

Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?

Cikin wadannan shekaru 60 da Sin ta shafe tana agazawa nahiyar Afirka ta fuskar kiwon lafiya, al’ummun nahiyar na ta jinjinawa moriyar da suka samu daga wannan aiki. Kuma a wannan gaba da Sin da kasashen Afirka ke kokarin gina al’umma mai makomar bai daya a sabon zamani, ciki har da fannin kula da lafiyar al’umma, tabbas likitocin Sin dake halartar ayyukan tallafawa al’umma a Afirka, na kan gaba wajen taimakawa cin nasarar wannan manufa.(Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ministocin Harkokin Wajen Saudiyya Da Iran Sun Gana Da Juna A Karon Farko A Beijing Karkashin Kokarin Sin 

Next Post

Yadda Tsarin Demokuradiyya Ya Samu Cikakkiyar Daraja A Kasar Sin

Related

Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin
Daga Birnin Sin

Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin

16 hours ago
Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?
Daga Birnin Sin

Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?

18 hours ago
Gwamnatin Hong Kong Ta Gudanar Da Bikin Cika Shekaru Biyar Da Kafuwar Dokar Tsaron Kasa Ta Yankin
Daga Birnin Sin

Gwamnatin Hong Kong Ta Gudanar Da Bikin Cika Shekaru Biyar Da Kafuwar Dokar Tsaron Kasa Ta Yankin

20 hours ago
Sin Ta Yi Matukar Allah Wadai Da Hare-Haren Da Amurka Ta Kaiwa Iran
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Matukar Allah Wadai Da Hare-Haren Da Amurka Ta Kaiwa Iran

21 hours ago
CMG Ya Ja Hankulan Baki A Dandalin Tattaunawar Tattalin Arziki Na Kasa Da Kasa Na St. Petersburg Karo Na 28 
Daga Birnin Sin

CMG Ya Ja Hankulan Baki A Dandalin Tattaunawar Tattalin Arziki Na Kasa Da Kasa Na St. Petersburg Karo Na 28 

2 days ago
Yankin Taiwan Ya Yi Taron Bikin Bauta Na Kakan Gargajiyar Sin Fuxi
Daga Birnin Sin

Yankin Taiwan Ya Yi Taron Bikin Bauta Na Kakan Gargajiyar Sin Fuxi

2 days ago
Next Post
Kasar Sin

Yadda Tsarin Demokuradiyya Ya Samu Cikakkiyar Daraja A Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

June 23, 2025
Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal

Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal

June 23, 2025
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Yakin Iran Da Isra’ila Ya Haifar Da Tashin Farashin Litar Man Fetur A Nijeriya

June 23, 2025
Hajji 2025: Kashi Na Farko Na Alhazan Abuja Sun Dawo Gida Nijeriya

Hajji 2025: Kashi Na Farko Na Alhazan Abuja Sun Dawo Gida Nijeriya

June 23, 2025
Gwamnan Abba Kabir Yusuf tare da Arch. Ali Hassan

Abba Ya Dace Ya Zama Gwamnan Kano Na Har Abada Ba Shekaru 8 Kaɗai Ba – Arch Ali Hassan

June 23, 2025
2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega

2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega

June 22, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

June 22, 2025
Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin

Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin

June 22, 2025
Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u

Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u

June 22, 2025
Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?

Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?

June 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.