• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Likitocin Sin Masu Aikin Jinya A Afirka Sun Zamo Jakadun Wanzar Da Kawance

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Likitocin Sin Masu Aikin Jinya A Afirka Sun Zamo Jakadun Wanzar Da Kawance
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A bana ne ake cika shekaru 60 tun bayan da kasar Sin ta fara aikewa da jami’an kiwon lafiya masu aikin jin kai zuwa kasashen Afirka daban daban. A sassa da dama a nahiyar Afirka, tawagogin likitocin na Sin sun yi rawar gani, wajen taimakawa mazauna wuraren, har ta kai ana kiran su da “Wakilai na gari kuma jakadun wanzar da kawance”, matsayin da ko shakka babu ya dace da godiyar da al’ummun nahiyar ke yiwa wadannan jami’ai masu aikin sadaukar da kai.

Tun bayan aikewa da tawagar irin wadannan likitoci na Sin zuwa kasar Aljeriya a watan Afrilun shekarar 1963, Sin ta ci gaba da aikewa da tawagogi daban daban zuwa Afirka. Baya ga kayan aiki da horaswa a fannin sanin makamar aiki da tawagogin ke samarwa a nahiyar.

  • Xi Ya Yi Kira Da A Nace Ga Alakar Sin Da Faransa Bisa Manyan Tsare-Tsare

Cikin sama da shekarun nan 60, Sin ta aike da tawagogin tallafin jinya mai kunshe da jimillar mambobi 30,000 zuwa kasashe da yankunan duniya 76, a sassan nahiyoyin duniya 5. Wasu alkaluman sun nuna cewa, adadin marasa lafiya da rukunonin likitocin Sin masu aikin jin kai suka yiwa jinya ya kai miliyan 290. Kaza lika a yanzu haka, wasu tawagogin likitocin na Sin na aiki a wurare 115 dake kasashe 57, kuma kusan rabin su na aiki ne a wurare masu wuyar kaiwa da yanayi mai tsanani.

Sanin kowa ne cewa nahiyar Afirka na shan fama da cututtuka masu yaduwa, kamar zazzabin cizon sauro ko Malaria, da Amai da gudanawa, da zazzabin shawara da sauran su, cututtukan da masana ke cewa karancin ababen more rayuwa ta fuskar kiwon lafiya, da kwararrun jami’an lafiya ne ke kara ta’azzara yaduwar su. Don haka ne ma rukunonin likitocin da Sin ke turawa suka dukufa, wajen samar da jinya ga dubun dubatar al’ummun nahiyar masu bukatar taimako.

Ko shakka babu rukunonin likitocin Sin sun cancanci yabo, bisa yadda suka gudanar da aikin tiyatar zuciya irin sa na farko a kasar Sudan, da dashen na’urar taimakawa zuciya irin sa na farko a Gambia, da aikin kwakwalwa irin sa na farko a kasar Benin, da dashen kafada a Mozambique da dai sauran su.

Labarai Masu Nasaba

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Cikin wadannan shekaru 60 da Sin ta shafe tana agazawa nahiyar Afirka ta fuskar kiwon lafiya, al’ummun nahiyar na ta jinjinawa moriyar da suka samu daga wannan aiki. Kuma a wannan gaba da Sin da kasashen Afirka ke kokarin gina al’umma mai makomar bai daya a sabon zamani, ciki har da fannin kula da lafiyar al’umma, tabbas likitocin Sin dake halartar ayyukan tallafawa al’umma a Afirka, na kan gaba wajen taimakawa cin nasarar wannan manufa.(Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ministocin Harkokin Wajen Saudiyya Da Iran Sun Gana Da Juna A Karon Farko A Beijing Karkashin Kokarin Sin 

Next Post

Yadda Tsarin Demokuradiyya Ya Samu Cikakkiyar Daraja A Kasar Sin

Related

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 
Daga Birnin Sin

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

10 hours ago
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
Daga Birnin Sin

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

11 hours ago
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba
Daga Birnin Sin

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

12 hours ago
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

13 hours ago
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 
Daga Birnin Sin

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

14 hours ago
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka
Daga Birnin Sin

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

16 hours ago
Next Post
Kasar Sin

Yadda Tsarin Demokuradiyya Ya Samu Cikakkiyar Daraja A Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.