• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lokaci Ya Yi Da Za A Bai Wa Mata Dama, Ina Goyon Bayan Takarar Binani A Adamawa —Buhari

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Siyasa
0
Lokaci Ya Yi Da Za A Bai Wa Mata Dama, Ina Goyon Bayan Takarar Binani A Adamawa —Buhari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, a ranar Litinin a garin Yola ta jihar Adamawa, ya ce, zabin Sanata Aisha Dahiru Ahmed Binani a matsayin Gwamnan Jihar a zaben 2023 da ke tafe zai bude sabon babi da ga ‘yan uwa mata a fadin kasar.

Buhari ya ce, yanzu fa ya kamata a bai wa mata gurabe su ma su fito a dama da su a bangaren gudanar da shugabanci a kasar nan.

  • An Sulhunta: Nuhu Ribadu Ya Hakura, Ya Bar Wa Aisha Binani Takarar Gwamnan APC A Adamawa
  • Kotun Daukaka Kara Ta Dawo Wa Da Aishatu Binani Takararta Ta Gwamna A Adamawa

Da yake jawabi a fadar Lamidon Adamawa a garin Yola, Shugaban kamar yadda da Kakakinsa Femi Adesina ya nakalto, ya ce, zai taimaka wa takarar Binani dari bisa dari kuma zai ci gaba da ba ta kwarin guiwa kan wannan matakin na neman gwamna da take yi.

“Mun zo nan ne domin mu tabbatar Sanata Binani ta zama zababbiyar gwamna ta farko da izinin Allah. Zabinta tamkar isar da sako ne ga Nijeriya da ma kasashen duniya.

“Ina muku godiya matuka a kan dukkan goyon bayanku. Ina fatan dukkaninku za ku goya mata baya ta kai ga nasara. Ga sauran ‘yan takara da suke bangaren adawa kuwa, ina musu fatan alheri.”

Labarai Masu Nasaba

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

A nasa jawabin, gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, ya gode wa shugaban kasa Muhammadu Buhari bisa ayyukan da ya shimfida a jihar daban-daban.

“Muna yi wa Shugaban kasa godiya kan ayyuka daban-daban da aka gudanar a jihar Adamawa. Za mu ci gaba da maka addu’a. .

“Ka yi matukar kokari sosai don ka yi abubuwa fiye da yadda ake tsammani a matsayinka na shugaba. Ina maka fatan alheri da fatan a kammala dukkanin yakin neman zabe cikin nasara,” cewar gwamnan.

Lamidon Adamawa, Alhaji Muhammadu Barkindo Aliyu Mustapha, shi ma godiya ya yi wa shugaban kasa bisa ayyukan raya jihar da ya gudanar.

Ya kuma yaba masa bisa irin nade-naden mukamai da ya bai wa ‘yan asalin jihar a cikin gwamnatinsa da suka hada da ministan babban birnin tarayya Abuja, Mohammed Musa Bello, sakataren Gwamnatin tarayya, Boss Mustapha da kuma shugaban hukumar yaki da fataucin miyagun kwayoyi NDLEA, Buba Marwa.

Sarkin ya kuma gode wa shugaban kasa Buhari kan amincewa da gina sabbin jami’o’i a jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AdamawaBinaniBuhari
ShareTweetSendShare
Previous Post

Turkashi: Aisha Bichi Ta Ce Jami’an Tsaron Farin Kaya Su Kamo Mata Abba Gida-Gida

Next Post

Sabon Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Zai Kai Ziyararsa Ta Farko Afirka

Related

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki
Manyan Labarai

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

3 days ago
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike
Siyasa

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

4 days ago
Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya
Siyasa

Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

1 week ago
‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027
Siyasa

‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027

2 weeks ago
Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi
Labarai

Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi

2 weeks ago
PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe
Siyasa

PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

3 weeks ago
Next Post
Sabon Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Zai Kai Ziyararsa Ta Farko Afirka

Sabon Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Zai Kai Ziyararsa Ta Farko Afirka

LABARAI MASU NASABA

Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.