• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lokaci Ya Yi Da Za A Bai Wa Mata Dama, Ina Goyon Bayan Takarar Binani A Adamawa —Buhari

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Siyasa
0
Lokaci Ya Yi Da Za A Bai Wa Mata Dama, Ina Goyon Bayan Takarar Binani A Adamawa —Buhari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, a ranar Litinin a garin Yola ta jihar Adamawa, ya ce, zabin Sanata Aisha Dahiru Ahmed Binani a matsayin Gwamnan Jihar a zaben 2023 da ke tafe zai bude sabon babi da ga ‘yan uwa mata a fadin kasar.

Buhari ya ce, yanzu fa ya kamata a bai wa mata gurabe su ma su fito a dama da su a bangaren gudanar da shugabanci a kasar nan.

  • An Sulhunta: Nuhu Ribadu Ya Hakura, Ya Bar Wa Aisha Binani Takarar Gwamnan APC A Adamawa
  • Kotun Daukaka Kara Ta Dawo Wa Da Aishatu Binani Takararta Ta Gwamna A Adamawa

Da yake jawabi a fadar Lamidon Adamawa a garin Yola, Shugaban kamar yadda da Kakakinsa Femi Adesina ya nakalto, ya ce, zai taimaka wa takarar Binani dari bisa dari kuma zai ci gaba da ba ta kwarin guiwa kan wannan matakin na neman gwamna da take yi.

“Mun zo nan ne domin mu tabbatar Sanata Binani ta zama zababbiyar gwamna ta farko da izinin Allah. Zabinta tamkar isar da sako ne ga Nijeriya da ma kasashen duniya.

“Ina muku godiya matuka a kan dukkan goyon bayanku. Ina fatan dukkaninku za ku goya mata baya ta kai ga nasara. Ga sauran ‘yan takara da suke bangaren adawa kuwa, ina musu fatan alheri.”

Labarai Masu Nasaba

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

A nasa jawabin, gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, ya gode wa shugaban kasa Muhammadu Buhari bisa ayyukan da ya shimfida a jihar daban-daban.

“Muna yi wa Shugaban kasa godiya kan ayyuka daban-daban da aka gudanar a jihar Adamawa. Za mu ci gaba da maka addu’a. .

“Ka yi matukar kokari sosai don ka yi abubuwa fiye da yadda ake tsammani a matsayinka na shugaba. Ina maka fatan alheri da fatan a kammala dukkanin yakin neman zabe cikin nasara,” cewar gwamnan.

Lamidon Adamawa, Alhaji Muhammadu Barkindo Aliyu Mustapha, shi ma godiya ya yi wa shugaban kasa bisa ayyukan raya jihar da ya gudanar.

Ya kuma yaba masa bisa irin nade-naden mukamai da ya bai wa ‘yan asalin jihar a cikin gwamnatinsa da suka hada da ministan babban birnin tarayya Abuja, Mohammed Musa Bello, sakataren Gwamnatin tarayya, Boss Mustapha da kuma shugaban hukumar yaki da fataucin miyagun kwayoyi NDLEA, Buba Marwa.

Sarkin ya kuma gode wa shugaban kasa Buhari kan amincewa da gina sabbin jami’o’i a jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AdamawaBinaniBuhari
ShareTweetSendShare
Previous Post

Turkashi: Aisha Bichi Ta Ce Jami’an Tsaron Farin Kaya Su Kamo Mata Abba Gida-Gida

Next Post

Sabon Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Zai Kai Ziyararsa Ta Farko Afirka

Related

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa
Labarai

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

2 days ago
Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027
Siyasa

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

2 days ago
NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC
Siyasa

NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC

2 days ago
Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu
Siyasa

Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

3 days ago
Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP
Siyasa

Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP

4 days ago
Dalilin Gwamnatin Kano Na Haramta Shirye-shiryen Siyasa Kai Tsaye
Siyasa

Dalilin Gwamnatin Kano Na Haramta Shirye-shiryen Siyasa Kai Tsaye

7 days ago
Next Post
Sabon Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Zai Kai Ziyararsa Ta Farko Afirka

Sabon Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Zai Kai Ziyararsa Ta Farko Afirka

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.