ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lokaci Ya Yi Da Za A Bai Wa Mata Dama, Ina Goyon Bayan Takarar Binani A Adamawa —Buhari

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Binani

Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, a ranar Litinin a garin Yola ta jihar Adamawa, ya ce, zabin Sanata Aisha Dahiru Ahmed Binani a matsayin Gwamnan Jihar a zaben 2023 da ke tafe zai bude sabon babi da ga ‘yan uwa mata a fadin kasar.

Buhari ya ce, yanzu fa ya kamata a bai wa mata gurabe su ma su fito a dama da su a bangaren gudanar da shugabanci a kasar nan.

  • An Sulhunta: Nuhu Ribadu Ya Hakura, Ya Bar Wa Aisha Binani Takarar Gwamnan APC A Adamawa
  • Kotun Daukaka Kara Ta Dawo Wa Da Aishatu Binani Takararta Ta Gwamna A Adamawa

Da yake jawabi a fadar Lamidon Adamawa a garin Yola, Shugaban kamar yadda da Kakakinsa Femi Adesina ya nakalto, ya ce, zai taimaka wa takarar Binani dari bisa dari kuma zai ci gaba da ba ta kwarin guiwa kan wannan matakin na neman gwamna da take yi.

ADVERTISEMENT

“Mun zo nan ne domin mu tabbatar Sanata Binani ta zama zababbiyar gwamna ta farko da izinin Allah. Zabinta tamkar isar da sako ne ga Nijeriya da ma kasashen duniya.

“Ina muku godiya matuka a kan dukkan goyon bayanku. Ina fatan dukkaninku za ku goya mata baya ta kai ga nasara. Ga sauran ‘yan takara da suke bangaren adawa kuwa, ina musu fatan alheri.”

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

A nasa jawabin, gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, ya gode wa shugaban kasa Muhammadu Buhari bisa ayyukan da ya shimfida a jihar daban-daban.

“Muna yi wa Shugaban kasa godiya kan ayyuka daban-daban da aka gudanar a jihar Adamawa. Za mu ci gaba da maka addu’a. .

“Ka yi matukar kokari sosai don ka yi abubuwa fiye da yadda ake tsammani a matsayinka na shugaba. Ina maka fatan alheri da fatan a kammala dukkanin yakin neman zabe cikin nasara,” cewar gwamnan.

Lamidon Adamawa, Alhaji Muhammadu Barkindo Aliyu Mustapha, shi ma godiya ya yi wa shugaban kasa bisa ayyukan raya jihar da ya gudanar.

Ya kuma yaba masa bisa irin nade-naden mukamai da ya bai wa ‘yan asalin jihar a cikin gwamnatinsa da suka hada da ministan babban birnin tarayya Abuja, Mohammed Musa Bello, sakataren Gwamnatin tarayya, Boss Mustapha da kuma shugaban hukumar yaki da fataucin miyagun kwayoyi NDLEA, Buba Marwa.

Sarkin ya kuma gode wa shugaban kasa Buhari kan amincewa da gina sabbin jami’o’i a jihar.

Binani
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Cafke Tsoho Mai Shekara 70 Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 8 Fyaɗe A Bauchi

MASU ALAKA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Binani
Siyasa

Muna Da Yan Takarar Gwamna A Jihohi 28 Don Shiga Zaben 2027

September 6, 2026
Next Post
Sabon Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Zai Kai Ziyararsa Ta Farko Afirka

Sabon Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Zai Kai Ziyararsa Ta Farko Afirka

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.