• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lokaci Ya Yi Da Za A Bai Wa Mata Dama, Ina Goyon Bayan Takarar Binani A Adamawa —Buhari

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Binani

Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, a ranar Litinin a garin Yola ta jihar Adamawa, ya ce, zabin Sanata Aisha Dahiru Ahmed Binani a matsayin Gwamnan Jihar a zaben 2023 da ke tafe zai bude sabon babi da ga ‘yan uwa mata a fadin kasar.

Buhari ya ce, yanzu fa ya kamata a bai wa mata gurabe su ma su fito a dama da su a bangaren gudanar da shugabanci a kasar nan.

  • An Sulhunta: Nuhu Ribadu Ya Hakura, Ya Bar Wa Aisha Binani Takarar Gwamnan APC A Adamawa
  • Kotun Daukaka Kara Ta Dawo Wa Da Aishatu Binani Takararta Ta Gwamna A Adamawa

Da yake jawabi a fadar Lamidon Adamawa a garin Yola, Shugaban kamar yadda da Kakakinsa Femi Adesina ya nakalto, ya ce, zai taimaka wa takarar Binani dari bisa dari kuma zai ci gaba da ba ta kwarin guiwa kan wannan matakin na neman gwamna da take yi.

“Mun zo nan ne domin mu tabbatar Sanata Binani ta zama zababbiyar gwamna ta farko da izinin Allah. Zabinta tamkar isar da sako ne ga Nijeriya da ma kasashen duniya.

“Ina muku godiya matuka a kan dukkan goyon bayanku. Ina fatan dukkaninku za ku goya mata baya ta kai ga nasara. Ga sauran ‘yan takara da suke bangaren adawa kuwa, ina musu fatan alheri.”

LABARAI MASU NASABA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

A nasa jawabin, gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, ya gode wa shugaban kasa Muhammadu Buhari bisa ayyukan da ya shimfida a jihar daban-daban.

“Muna yi wa Shugaban kasa godiya kan ayyuka daban-daban da aka gudanar a jihar Adamawa. Za mu ci gaba da maka addu’a. .

“Ka yi matukar kokari sosai don ka yi abubuwa fiye da yadda ake tsammani a matsayinka na shugaba. Ina maka fatan alheri da fatan a kammala dukkanin yakin neman zabe cikin nasara,” cewar gwamnan.

Lamidon Adamawa, Alhaji Muhammadu Barkindo Aliyu Mustapha, shi ma godiya ya yi wa shugaban kasa bisa ayyukan raya jihar da ya gudanar.

Ya kuma yaba masa bisa irin nade-naden mukamai da ya bai wa ‘yan asalin jihar a cikin gwamnatinsa da suka hada da ministan babban birnin tarayya Abuja, Mohammed Musa Bello, sakataren Gwamnatin tarayya, Boss Mustapha da kuma shugaban hukumar yaki da fataucin miyagun kwayoyi NDLEA, Buba Marwa.

Sarkin ya kuma gode wa shugaban kasa Buhari kan amincewa da gina sabbin jami’o’i a jihar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas
Labarai

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

October 2, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

September 28, 2025
Next Post
Sabon Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Zai Kai Ziyararsa Ta Farko Afirka

Sabon Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Zai Kai Ziyararsa Ta Farko Afirka

LABARAI MASU NASABA

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.