• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ma’aikatar kula da kasuwanci ta kasar Sin ta bayyana a jiya Laraba cewa, don tabbatar da matsaya daya da manyan jami’ai masu kula da cinikayya da tattalin arziki na kasashen Sin da Amurka suka cimma, bisa “dokar yaki da takunkumaman kasashen waje ta kasar Sin” da “doka kan jerin kamfanoni da daidaikun mutane da Sin ta haramta huldar cinikayya da su”, an dakatar da jerin matakan haramta cinikayya da Sin ta sanar da dauka kan wasu kamfanonin Amurka a ranar 4 ga watan Afrilu na tsawon wa’adin kwanaki 90, an kuma dakatar da matakan da ta dauka a ranar 9, inda dukkan dakatarwar suka fara aiki daga jiya Laraba, 14 ga watan nan da muke ciki.

A ranekun 4 da 9 ga watan Afrilun bana ne kasar Sin ta fara amfani da tsarin jerin kamfanoni ko daidaikun mutane da ba ta amince da su ba wato ta haramta huldar cinikayya da su, bisa dokar yaki da takunkumin da kasashen ketare ke kakkaba mata da tanade-tanaden wannan tsari da sauran abubuwan dake da nasaba da shi, inda ta shigar da kamfanoni 17 na Amurka cikin wannan jerin, tare da haramta musu gudanar da cinikin shige da fice da Sin ko zuba jari a kasar.

  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

Ban da haka, kakakin ma’aikatar ya ce, bisa tanade-tanaden dake cikin tsarin jerin kamfanoni da daidaikun mutanen da Sin ba ta amince da su ba, kamfanonin Sin suna iya mika rokonsu na neman izinin yin ciniki da wadannan kamfanoni, bisa binciken da aka yi bisa wannan tsari.

Kakakin ya kara da cewa, bisa tanadin doka ko shari’ar dake da nasaba da kayyade fitar da kayayyaki zuwa ketare, ma’aikatarsa ta gabatar da sanarwoyi mai lamba 21 da mai 22 a ranekun 4 da 9 ga watan Afrilun bana, inda ta shigar da kamfanoni 28 cikin jerin kamfanonin da Sin ta kayyade fitar musu kayayyakin amfanin yau da kullum, wadanda za a iya yin amfani da su a bangaren aikin soja. Kuma daga jiya Laraba, cikin kwanaki 90 masu zuwa, za a dakatar da wadannan matakai, don tabbatar da matsaya daya da shugabannin kasashen Sin da Amurka suka cimma.

Dadin dadawa, kakakin ya ce, idan masu cinikin fitar da kayayyaki zuwa ketare a nan kasar Sin suna da bukatar fitarwa wadannan kamfanoni 28 dake cikin jerin sunayen kayayyakin da aka ambata, to za su iya gabatarwa ma’aikatar kasuwanci ta Sin rokonsu bisa doka da shari’a, kuma ma’aikatar za ta ba su izini bayan gudanar da bincike. (Amina Xu)

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

Next Post

Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025

Related

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

7 hours ago
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu
Daga Birnin Sin

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

8 hours ago
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

9 hours ago
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere
Daga Birnin Sin

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

11 hours ago
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

12 hours ago
Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa
Daga Birnin Sin

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

13 hours ago
Next Post
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.