Ma’aikatar kula da kasuwanci ta kasar Sin ta bayyana a jiya Laraba cewa, don tabbatar da matsaya daya da manyan jami’ai masu kula da cinikayya da tattalin arziki na kasashen Sin da Amurka suka cimma, bisa “dokar yaki da takunkumaman kasashen waje ta kasar Sin” da “doka kan jerin kamfanoni da daidaikun mutane da Sin ta haramta huldar cinikayya da su”, an dakatar da jerin matakan haramta cinikayya da Sin ta sanar da dauka kan wasu kamfanonin Amurka a ranar 4 ga watan Afrilu na tsawon wa’adin kwanaki 90, an kuma dakatar da matakan da ta dauka a ranar 9, inda dukkan dakatarwar suka fara aiki daga jiya Laraba, 14 ga watan nan da muke ciki.
A ranekun 4 da 9 ga watan Afrilun bana ne kasar Sin ta fara amfani da tsarin jerin kamfanoni ko daidaikun mutane da ba ta amince da su ba wato ta haramta huldar cinikayya da su, bisa dokar yaki da takunkumin da kasashen ketare ke kakkaba mata da tanade-tanaden wannan tsari da sauran abubuwan dake da nasaba da shi, inda ta shigar da kamfanoni 17 na Amurka cikin wannan jerin, tare da haramta musu gudanar da cinikin shige da fice da Sin ko zuba jari a kasar.
- ‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi
- ‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi
Ban da haka, kakakin ma’aikatar ya ce, bisa tanade-tanaden dake cikin tsarin jerin kamfanoni da daidaikun mutanen da Sin ba ta amince da su ba, kamfanonin Sin suna iya mika rokonsu na neman izinin yin ciniki da wadannan kamfanoni, bisa binciken da aka yi bisa wannan tsari.
Kakakin ya kara da cewa, bisa tanadin doka ko shari’ar dake da nasaba da kayyade fitar da kayayyaki zuwa ketare, ma’aikatarsa ta gabatar da sanarwoyi mai lamba 21 da mai 22 a ranekun 4 da 9 ga watan Afrilun bana, inda ta shigar da kamfanoni 28 cikin jerin kamfanonin da Sin ta kayyade fitar musu kayayyakin amfanin yau da kullum, wadanda za a iya yin amfani da su a bangaren aikin soja. Kuma daga jiya Laraba, cikin kwanaki 90 masu zuwa, za a dakatar da wadannan matakai, don tabbatar da matsaya daya da shugabannin kasashen Sin da Amurka suka cimma.
Dadin dadawa, kakakin ya ce, idan masu cinikin fitar da kayayyaki zuwa ketare a nan kasar Sin suna da bukatar fitarwa wadannan kamfanoni 28 dake cikin jerin sunayen kayayyakin da aka ambata, to za su iya gabatarwa ma’aikatar kasuwanci ta Sin rokonsu bisa doka da shari’a, kuma ma’aikatar za ta ba su izini bayan gudanar da bincike. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp