• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Sin Da Turai Da Su Aiwatar Da Takara Mai Tsafta Don Cimma Nasara Tare

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Sin Da Turai Da Su Aiwatar Da Takara Mai Tsafta Don Cimma Nasara Tare
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ma’aikatar kasuwanci ta kasar Sin, ta gudanar da tarukan tattaunawa na kamfanonin Sin a Sifaniya, da Portugal, da Girka, da sauran wasu kasashen Turai, inda aka saurari muryoyi, da bukatun kamfanoni, da kungiyoyin kasuwanci na Sin dake kasashen Turai, kana bangaren Sin ya yi kira ga bangarorin Sin da na Turai da su warware takaddamar tattalin arziki, da cinikayya ta hanyar tattaunawa.

Kaza lika bangaren na Sin ya bukaci a kula da bukatun bangarorin biyu, don kaucewa habakar ricikin cinikayya. Kana Sin ta yi kira da a gudanar da hadin gwiwa don cimma nasara tare tsakanin bangarorin biyu, kuma ta yi maraba da gudanar da takara ta gari.

  • Abin Da Ya Sa Nake Rungumar Ɗana Ina Wakar Soyayya – Tsohuwar Matar Adam Zango, Amina
  • Ma’aikata Sun Nemi Gwamnoni Su Zaftare Albashin Su Don Biyan Mafi Karancin Albashi

Yayin tarukan, wasu wakilan kamfanonin Sin sun bayyana cewa, a kwanan nan, kungiyar tarayyar Turai wato EU, ta ci gaba da yakar kamfanonin Sin, bisa hujjar wai “Yin Gasa Cikin Adalci”.

Bugu da kari, bisa binciken da kungiyar kasuwancin Sin ta EU ta yi, a shekaru hudu a jere, ra’ayin kamfanonin Sin game da yanayin kasuwanci a EU yana kara yin kasa, wanda ya dami mutane sosai.

Game da hakan, ministan kasuwancin Sin Wang Wentao, yayin da yake shugabantar taron masu ruwa da tsaki na kamfanonin Sin a birnin Lisbon fadar mulkin Portugal, ya bayyana cewa, zargin da wasu kasashe ke yi wa Sin na “Karancin adalci a takara”, ba shi da tushe ko kadan. Ya ce, takara ta adalci ita ce fahimtar juna tsakanin kasashen duniya, kuma ginshiki ce ta mu’amalar kasa da kasa, wadda ba za a bar wasu kasashe kalilan su yi iko da ita ba.

Labarai Masu Nasaba

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

A zahiri, takara ta adalci, ya kamata ta kasance ta hanyar kokari, da himma domin cimma nasara, ba tare da neman hanyar takalar sauran sassa ba. Ya kamata ta kasance hanyar bude kofa da hadin gwiwa, da samun moriyar juna cikin daidaito, maimakon a rufe kai, da kebewa, ko hada wani gungu.

Kaza lika, ya kamata takara mai tsafta ta kasance ta bin ka’idojin da aka riga aka amince da su tsakanin kasa da kasa, maimakon a karya su, ko canza su bisa ra’ayin kashin kai. Sin tana maraba da hadin gwiwa da cimma nasara tare, amma ba ta tsoron takara, kana tana maraba da takara ta gari, tare da adawa da takara mai nufin hana ci gaba. (Safiyah Ma)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kansila Ya Ɗauki Nauyin Karatun Ɗalibai 120 A Kano

Next Post

Zamu Ba Wa Maraɗa Kunya A Wasanmu Na Gaba Da Ƙasar Benin – Finidi

Related

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

10 hours ago
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

11 hours ago
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12
Daga Birnin Sin

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

12 hours ago
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana
Daga Birnin Sin

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

13 hours ago
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

14 hours ago
Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa
Daga Birnin Sin

Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa

15 hours ago
Next Post
Zamu Ba Wa Maraɗa Kunya A Wasanmu Na Gaba Da Ƙasar Benin – Finidi

Zamu Ba Wa Maraɗa Kunya A Wasanmu Na Gaba Da Ƙasar Benin - Finidi

LABARAI MASU NASABA

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

August 23, 2025
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

August 23, 2025
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.