• English
  • Business News
Thursday, July 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ma’anar Sabon Tsarin Hadin Kan Mambobin Brics a Sabon Zamani Ga Dunkulewar Kasashe Masu Tasowa

by Sulaiman
6 hours ago
in Daga Birnin Sin
0
Ma’anar Sabon Tsarin Hadin Kan Mambobin Brics a Sabon Zamani Ga Dunkulewar Kasashe Masu Tasowa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An rufe taron shugabannin BRICS karo na 17 a Rio de Janeiro hedkwatar Brazil a ran 7 ga watan nan da muke ciki agogon kasar. Taron ya fitar da sanarwar Rio de Janeiro, inda aka kai ga matsaya daya kan batun raya fasahar AI da tinkarar sauyin yanayi da dai sauran bangarori.

 

An yi wannan taro ne a daidai lokacin da duniya ke fuskantar dimbin sauye-sauye. Mabambantan bangarori na ganin akwai matukar bukatar yi wa tsarin daidaita harkokin duniya kwaskwarima cikin gaggawa. To, wace rawa kasar Sin za ta taka game da wannan batun, duba da matsayinta na babban ginshiki a BRICS?

  • Akwai Bukatar Sin Da Masar Su Zurfafa Hadin Gwiwa Domin Kare Muradunsu
  • Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

Bari mu yi bayani. Kwanan baya, Sin da sauran mambobin BRICS sun yi iyakacin kokarin tabbatar da shimfida zaman lafiya a duniya. Wannan karo kuwa, Sin ta nanata wajibcin kasashe mambobin BRICS su jagoranci tabbatar da adalci, kana su yi kokarin tabbatar da da’a da adalci, sannan su karfafa magance rigingimu ta hanyar zaman lafiya, da warware matsaloli bisa gaskiya da hakkin abubuwan da ke faruwa.

 

Labarai Masu Nasaba

UNHRC Ta Zartas Da Kudurin Sin Kan Kiyaye Hakkin Dan Adam Ta Hanyar Samun Ci Gaba

An Fara Taron Nishan Karo Na 11 Game Da Wayewar Kai A Duniya

Game da koma bayan tattalin arziki da duniya ke fuskanta, ana matukar bukatar bullo da sabbin hanyoyin samun bunkasa. Shi ya sa, yin kirkire-kirkire da habaka hanyoyin samun bunkasa, ya zama mataki mafi jawo hankula daga cikin tsarin hadin gwiwar mambobin BRICS. Sin ta sanar a wannan taro cewa, za ta kafa cibiyar nazarin sabon karfin samar da hajoji da hidimomi masu karko ta Sin da kasashen mambobin BRICS.

 

Kazalika, game da babakeren da Amurka ke nunawa, mambobin BRICS sun yi kira da a kiyaye ra’ayin kasancewar mabambantan bangarori a duniya da gaggauta kafa kyakkyawan tsari da dokar tattalin arziki da cinikin duniya mai adalci da bude kofa. Albarkacin cika shekaru 10 da kafuwar bankin NDB na BRICS, Sin na goyon bayan bankin da ya kara karfinsa don daga matsayin hadin gwiwar kasa da kasa a bangaren harkar hada-hadar kudaden duniya.

Dadin dadawa, a shekaru 20 da suka gabata, tsarin hadin kan BRICS na zama muhimminyar alamar dunkulewa da hadin gwiwar kasashe masu tasowa. Sin za ta ci gaba da daukar matakan da suka fi dacewa nan gaba, don gaggauta bunkasar wannan nagartaccen tsari da bai wa duk fadin duniya tabbaci, wadda ke fuskantar dimbin matsaloli da dimbin kalubale da sauye-sauye. (Amina Xu)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wasanmu Da Real Madrid Zai Kasance Na Musamman – Luis Enrique

Next Post

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 13 A Neja

Related

UNHRC Ta Zartas Da Kudurin Sin Kan Kiyaye Hakkin Dan Adam Ta Hanyar Samun Ci Gaba
Daga Birnin Sin

UNHRC Ta Zartas Da Kudurin Sin Kan Kiyaye Hakkin Dan Adam Ta Hanyar Samun Ci Gaba

3 hours ago
An Fara Taron Nishan Karo Na 11 Game Da Wayewar Kai A Duniya
Daga Birnin Sin

An Fara Taron Nishan Karo Na 11 Game Da Wayewar Kai A Duniya

4 hours ago
An Yi Hasashen Karuwar Tattalin Arzikin Kasar Sin Za Ta Zarce Yuan Tiriliyan 35 Tsakanin 2021 Zuwa 2025
Daga Birnin Sin

An Yi Hasashen Karuwar Tattalin Arzikin Kasar Sin Za Ta Zarce Yuan Tiriliyan 35 Tsakanin 2021 Zuwa 2025

5 hours ago
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Kara Kamfanoni 8 Na Yankin Taiwan Cikin Jerin Wadanda Aka Takaita Sayar Musu Kayayyaki
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Kara Kamfanoni 8 Na Yankin Taiwan Cikin Jerin Wadanda Aka Takaita Sayar Musu Kayayyaki

7 hours ago
Mai Tsoron Ta Mutu, Shi Yake Maho
Daga Birnin Sin

Mai Tsoron Ta Mutu, Shi Yake Maho

8 hours ago
Akwai Bukatar Sin Da Masar Su Zurfafa Hadin Gwiwa Domin Kare Muradunsu
Daga Birnin Sin

Akwai Bukatar Sin Da Masar Su Zurfafa Hadin Gwiwa Domin Kare Muradunsu

9 hours ago
Next Post
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 13 A Neja

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 13 A Neja

LABARAI MASU NASABA

UNHRC Ta Zartas Da Kudurin Sin Kan Kiyaye Hakkin Dan Adam Ta Hanyar Samun Ci Gaba

UNHRC Ta Zartas Da Kudurin Sin Kan Kiyaye Hakkin Dan Adam Ta Hanyar Samun Ci Gaba

July 9, 2025
Har Yanzu A Cikin PDP Nake, Ba Zan Koma APC Ko ADC Ba – Gwamnan Zamfara

Har Yanzu A Cikin PDP Nake, Ba Zan Koma APC Ko ADC Ba – Gwamnan Zamfara

July 9, 2025
An Fara Taron Nishan Karo Na 11 Game Da Wayewar Kai A Duniya

An Fara Taron Nishan Karo Na 11 Game Da Wayewar Kai A Duniya

July 9, 2025
EFCC Ta Kama Ƴan Ƙasashen Waje 146 Kan Laifukan Zambar Kuɗaɗe

EFCC Ta Kama Ƴan Ƙasashen Waje 146 Kan Laifukan Zambar Kuɗaɗe

July 9, 2025
An Yi Hasashen Karuwar Tattalin Arzikin Kasar Sin Za Ta Zarce Yuan Tiriliyan 35 Tsakanin 2021 Zuwa 2025

An Yi Hasashen Karuwar Tattalin Arzikin Kasar Sin Za Ta Zarce Yuan Tiriliyan 35 Tsakanin 2021 Zuwa 2025

July 9, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 13 A Neja

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 13 A Neja

July 9, 2025
Ma’anar Sabon Tsarin Hadin Kan Mambobin Brics a Sabon Zamani Ga Dunkulewar Kasashe Masu Tasowa

Ma’anar Sabon Tsarin Hadin Kan Mambobin Brics a Sabon Zamani Ga Dunkulewar Kasashe Masu Tasowa

July 9, 2025
Wasanmu Da Real Madrid Zai Kasance Na Musamman – Luis Enrique

Wasanmu Da Real Madrid Zai Kasance Na Musamman – Luis Enrique

July 9, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Kara Kamfanoni 8 Na Yankin Taiwan Cikin Jerin Wadanda Aka Takaita Sayar Musu Kayayyaki

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Kara Kamfanoni 8 Na Yankin Taiwan Cikin Jerin Wadanda Aka Takaita Sayar Musu Kayayyaki

July 9, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 30 A Katsina

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 30 A Katsina

July 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.