• English
  • Business News
Monday, October 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Magance Bala’o’i: Gwamna Lawal Ya Jaddada Ƙudirin Gwamnatin Zamfara Na Ci Gaba Da Haɗin Gwiwa Da NEMA

by Sulaiman
3 hours ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya tabbatar da aniyar gwamnatin sa ta ci gaba da haɗa kai da Hukumar Kai Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) wajen inganta tsarin daƙile bala’o’i da haɗurra a faɗin jihar.

 

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ranar Litinin, 13 ga watan Oktoba, tn bayyana cewa Gwamna Lawal ya halarci bikin Ranar Ƙasa da Ƙasa ta Rage Haɗarin Bala’o’i ta shekarar 2025, da kuma ƙaddamar da sabbin tsare-tsare da suka shafi wannan fanni, wanda aka gudanar a cibiyar taro ta NAF da ke Abuja.

A wajen taron, Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, GCON, ne ya jagoranci ƙaddamar da Shirin Tsare-Tsaren NEMA na Shekaru Biyar (2025–2029), da Manufar Rage Haɗarin Bala’o’i (2025–2030), da kuma Shirin Ayyuka na Shekaru Uku (2025–2028), ƙarƙashin taken: “Fund Resilience, Not Disaster” – wato, kuɗaɗe su tallafa wa juriya, ba bala’o’i ba.

 

LABARAI MASU NASABA

Zargin Batanci: An Sasanta Da Malam Lawal Triumph Da Majalisar Shura Ta Kano

Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

A jawabin sa, Gwamna Lawal, ya yaba wa NEMA bisa shirya wannan muhimmin taro da kuma jajircewarsu wajen gina tsarin rage haɗarin bala’o’i a Nijeriya.

 

Ya ce, “Bala’o’i kan zo cikin tsarin da ke jawo juna — bala’i ɗaya na iya haifar da wani. Wannan ya nuna cewa babu haɗari da ke zaman kansa; duk suna da alaƙa da juna, kuma magance su na buƙatar tsari mai ma’ana da haɗin kai.”

 

Gwamnan ya ƙara da cewa, yayin da aka ƙaddamar da wannan sabon shiri na shekaru biyar, akwai buƙatar kowane ɓangare ya zurfafa haɗin gwiwa, domin a tabbatar da cewa babu wanda aka bari a baya wajen gina ƙasa mai juriya da aminci.

 

A cewar sa, taken bana na “Fund Resilience, Not Disasters” ya zama wajibi a juya shi zuwa tsare-tsare na zahiri da za su tabbatar da ɗorewar kuɗaɗen da ake warewa don kula da bala’o’i, ganin cewa wannan fanni yana ta canjawa lokaci zuwa lokaci.

 

Gwamna Lawal ya kuma bayyana irin ƙalubalen da Jihar Zamfara ke fuskanta, ciki har da matsalar tsaro, gobara, ambaliyar ruwa, ruftawar ramin haƙar ma’adinai, da sauran tasirin sauyin yanayi. Duk da haka, ya yaba wa NEMA bisa kasancewa tamkar ginshiƙi wajen tallafa wa jihar a duk lokacin da ake fuskantar irin waɗannan matsaloli.

 

Ya ce, “Mun ƙarfafa hukumar mu ta Zamfara Emergency Management Agency (ZEMA) da ƙarin iko domin inganta amsawa kiran gaggawa ga bala’o’i. Muna kuma haɗa tsarin kula da haɗurra cikin tafiyar da gwamnati ta hanyar gargaɗi da wuri, haɗin kai da al’umma, da gyaran cibiyoyi — domin mu yi imani cewa juriya mai ɗorewa tana farawa daga matakin jiha.”

 

A ƙarshe, Gwamna Lawal ya miƙa godiya ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, GCFR, bisa jagorancinsa a waɗannan lokutan ƙalubale, tare da gode wa Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, GCON, da kuma Darakta Janar ta NEMA, Hajiya Zubaida Umar, bisa haɗin gwiwa da taimako da suke bai wa Zamfara don fuskantar matsalolinta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Zargin Batanci: An Sasanta Da Malam Lawal Triumph Da Majalisar Shura Ta Kano
Labarai

Zargin Batanci: An Sasanta Da Malam Lawal Triumph Da Majalisar Shura Ta Kano

October 13, 2025
Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano
Manyan Labarai

Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

October 13, 2025
Asuu
Labarai

Ba Bu Dalilin Da ASUU Za Ta Fara Yajin Aiki, An Biya Duk Buƙatunsu – Ministan Ilimi 

October 13, 2025
Next Post
Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Barazanar Amurka Ta Kara Haraji Game Da Batun Ma’adanan Farin Karfe Ba Hanya Ce Mai Bullewa Ba

Barazanar Amurka Ta Kara Haraji Game Da Batun Ma’adanan Farin Karfe Ba Hanya Ce Mai Bullewa Ba

October 13, 2025
Zargin Batanci: An Sasanta Da Malam Lawal Triumph Da Majalisar Shura Ta Kano

Zargin Batanci: An Sasanta Da Malam Lawal Triumph Da Majalisar Shura Ta Kano

October 13, 2025
Hada-Hadar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso 4% Cikin Watanni Tara Na Farkon Bana

Hada-Hadar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso 4% Cikin Watanni Tara Na Farkon Bana

October 13, 2025
Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

October 13, 2025
Magance Bala’o’i: Gwamna Lawal Ya Jaddada Ƙudirin Gwamnatin Zamfara Na Ci Gaba Da Haɗin Gwiwa Da NEMA

Magance Bala’o’i: Gwamna Lawal Ya Jaddada Ƙudirin Gwamnatin Zamfara Na Ci Gaba Da Haɗin Gwiwa Da NEMA

October 13, 2025
Asuu

Ba Bu Dalilin Da ASUU Za Ta Fara Yajin Aiki, An Biya Duk Buƙatunsu – Ministan Ilimi 

October 13, 2025
hisba

Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano

October 13, 2025
Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

October 13, 2025
Nijeriya

Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista

October 13, 2025
Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano

Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano

October 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.