ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Magance Bala’o’i: Gwamna Lawal Ya Jaddada Ƙudirin Gwamnatin Zamfara Na Ci Gaba Da Haɗin Gwiwa Da NEMA

by Sulaiman
11 months ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya tabbatar da aniyar gwamnatin sa ta ci gaba da haɗa kai da Hukumar Kai Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) wajen inganta tsarin daƙile bala’o’i da haɗurra a faɗin jihar.

 

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ranar Litinin, 13 ga watan Oktoba, tn bayyana cewa Gwamna Lawal ya halarci bikin Ranar Ƙasa da Ƙasa ta Rage Haɗarin Bala’o’i ta shekarar 2025, da kuma ƙaddamar da sabbin tsare-tsare da suka shafi wannan fanni, wanda aka gudanar a cibiyar taro ta NAF da ke Abuja.

ADVERTISEMENT

A wajen taron, Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, GCON, ne ya jagoranci ƙaddamar da Shirin Tsare-Tsaren NEMA na Shekaru Biyar (2025–2029), da Manufar Rage Haɗarin Bala’o’i (2025–2030), da kuma Shirin Ayyuka na Shekaru Uku (2025–2028), ƙarƙashin taken: “Fund Resilience, Not Disaster” – wato, kuɗaɗe su tallafa wa juriya, ba bala’o’i ba.

 

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

A jawabin sa, Gwamna Lawal, ya yaba wa NEMA bisa shirya wannan muhimmin taro da kuma jajircewarsu wajen gina tsarin rage haɗarin bala’o’i a Nijeriya.

 

Ya ce, “Bala’o’i kan zo cikin tsarin da ke jawo juna — bala’i ɗaya na iya haifar da wani. Wannan ya nuna cewa babu haɗari da ke zaman kansa; duk suna da alaƙa da juna, kuma magance su na buƙatar tsari mai ma’ana da haɗin kai.”

 

Gwamnan ya ƙara da cewa, yayin da aka ƙaddamar da wannan sabon shiri na shekaru biyar, akwai buƙatar kowane ɓangare ya zurfafa haɗin gwiwa, domin a tabbatar da cewa babu wanda aka bari a baya wajen gina ƙasa mai juriya da aminci.

 

A cewar sa, taken bana na “Fund Resilience, Not Disasters” ya zama wajibi a juya shi zuwa tsare-tsare na zahiri da za su tabbatar da ɗorewar kuɗaɗen da ake warewa don kula da bala’o’i, ganin cewa wannan fanni yana ta canjawa lokaci zuwa lokaci.

 

Gwamna Lawal ya kuma bayyana irin ƙalubalen da Jihar Zamfara ke fuskanta, ciki har da matsalar tsaro, gobara, ambaliyar ruwa, ruftawar ramin haƙar ma’adinai, da sauran tasirin sauyin yanayi. Duk da haka, ya yaba wa NEMA bisa kasancewa tamkar ginshiƙi wajen tallafa wa jihar a duk lokacin da ake fuskantar irin waɗannan matsaloli.

 

Ya ce, “Mun ƙarfafa hukumar mu ta Zamfara Emergency Management Agency (ZEMA) da ƙarin iko domin inganta amsawa kiran gaggawa ga bala’o’i. Muna kuma haɗa tsarin kula da haɗurra cikin tafiyar da gwamnati ta hanyar gargaɗi da wuri, haɗin kai da al’umma, da gyaran cibiyoyi — domin mu yi imani cewa juriya mai ɗorewa tana farawa daga matakin jiha.”

 

A ƙarshe, Gwamna Lawal ya miƙa godiya ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, GCFR, bisa jagorancinsa a waɗannan lokutan ƙalubale, tare da gode wa Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, GCON, da kuma Darakta Janar ta NEMA, Hajiya Zubaida Umar, bisa haɗin gwiwa da taimako da suke bai wa Zamfara don fuskantar matsalolinta.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara
  • Sulaiman
    Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

MASU ALAKA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
Manyan Labarai

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
Next Post
Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.