ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Magance Bala’o’i: Gwamna Lawal Ya Jaddada Ƙudirin Gwamnatin Zamfara Na Ci Gaba Da Haɗin Gwiwa Da NEMA

by Sulaiman
8 months ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya tabbatar da aniyar gwamnatin sa ta ci gaba da haɗa kai da Hukumar Kai Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) wajen inganta tsarin daƙile bala’o’i da haɗurra a faɗin jihar.

 

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ranar Litinin, 13 ga watan Oktoba, tn bayyana cewa Gwamna Lawal ya halarci bikin Ranar Ƙasa da Ƙasa ta Rage Haɗarin Bala’o’i ta shekarar 2025, da kuma ƙaddamar da sabbin tsare-tsare da suka shafi wannan fanni, wanda aka gudanar a cibiyar taro ta NAF da ke Abuja.

ADVERTISEMENT

A wajen taron, Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, GCON, ne ya jagoranci ƙaddamar da Shirin Tsare-Tsaren NEMA na Shekaru Biyar (2025–2029), da Manufar Rage Haɗarin Bala’o’i (2025–2030), da kuma Shirin Ayyuka na Shekaru Uku (2025–2028), ƙarƙashin taken: “Fund Resilience, Not Disaster” – wato, kuɗaɗe su tallafa wa juriya, ba bala’o’i ba.

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

A jawabin sa, Gwamna Lawal, ya yaba wa NEMA bisa shirya wannan muhimmin taro da kuma jajircewarsu wajen gina tsarin rage haɗarin bala’o’i a Nijeriya.

 

Ya ce, “Bala’o’i kan zo cikin tsarin da ke jawo juna — bala’i ɗaya na iya haifar da wani. Wannan ya nuna cewa babu haɗari da ke zaman kansa; duk suna da alaƙa da juna, kuma magance su na buƙatar tsari mai ma’ana da haɗin kai.”

 

Gwamnan ya ƙara da cewa, yayin da aka ƙaddamar da wannan sabon shiri na shekaru biyar, akwai buƙatar kowane ɓangare ya zurfafa haɗin gwiwa, domin a tabbatar da cewa babu wanda aka bari a baya wajen gina ƙasa mai juriya da aminci.

 

A cewar sa, taken bana na “Fund Resilience, Not Disasters” ya zama wajibi a juya shi zuwa tsare-tsare na zahiri da za su tabbatar da ɗorewar kuɗaɗen da ake warewa don kula da bala’o’i, ganin cewa wannan fanni yana ta canjawa lokaci zuwa lokaci.

 

Gwamna Lawal ya kuma bayyana irin ƙalubalen da Jihar Zamfara ke fuskanta, ciki har da matsalar tsaro, gobara, ambaliyar ruwa, ruftawar ramin haƙar ma’adinai, da sauran tasirin sauyin yanayi. Duk da haka, ya yaba wa NEMA bisa kasancewa tamkar ginshiƙi wajen tallafa wa jihar a duk lokacin da ake fuskantar irin waɗannan matsaloli.

 

Ya ce, “Mun ƙarfafa hukumar mu ta Zamfara Emergency Management Agency (ZEMA) da ƙarin iko domin inganta amsawa kiran gaggawa ga bala’o’i. Muna kuma haɗa tsarin kula da haɗurra cikin tafiyar da gwamnati ta hanyar gargaɗi da wuri, haɗin kai da al’umma, da gyaran cibiyoyi — domin mu yi imani cewa juriya mai ɗorewa tana farawa daga matakin jiha.”

 

A ƙarshe, Gwamna Lawal ya miƙa godiya ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, GCFR, bisa jagorancinsa a waɗannan lokutan ƙalubale, tare da gode wa Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, GCON, da kuma Darakta Janar ta NEMA, Hajiya Zubaida Umar, bisa haɗin gwiwa da taimako da suke bai wa Zamfara don fuskantar matsalolinta.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.