ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Magance Bala’o’i: Gwamna Lawal Ya Jaddada Ƙudirin Gwamnatin Zamfara Na Ci Gaba Da Haɗin Gwiwa Da NEMA

by Sulaiman
8 months ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya tabbatar da aniyar gwamnatin sa ta ci gaba da haɗa kai da Hukumar Kai Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) wajen inganta tsarin daƙile bala’o’i da haɗurra a faɗin jihar.

 

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ranar Litinin, 13 ga watan Oktoba, tn bayyana cewa Gwamna Lawal ya halarci bikin Ranar Ƙasa da Ƙasa ta Rage Haɗarin Bala’o’i ta shekarar 2025, da kuma ƙaddamar da sabbin tsare-tsare da suka shafi wannan fanni, wanda aka gudanar a cibiyar taro ta NAF da ke Abuja.

ADVERTISEMENT

A wajen taron, Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, GCON, ne ya jagoranci ƙaddamar da Shirin Tsare-Tsaren NEMA na Shekaru Biyar (2025–2029), da Manufar Rage Haɗarin Bala’o’i (2025–2030), da kuma Shirin Ayyuka na Shekaru Uku (2025–2028), ƙarƙashin taken: “Fund Resilience, Not Disaster” – wato, kuɗaɗe su tallafa wa juriya, ba bala’o’i ba.

 

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

A jawabin sa, Gwamna Lawal, ya yaba wa NEMA bisa shirya wannan muhimmin taro da kuma jajircewarsu wajen gina tsarin rage haɗarin bala’o’i a Nijeriya.

 

Ya ce, “Bala’o’i kan zo cikin tsarin da ke jawo juna — bala’i ɗaya na iya haifar da wani. Wannan ya nuna cewa babu haɗari da ke zaman kansa; duk suna da alaƙa da juna, kuma magance su na buƙatar tsari mai ma’ana da haɗin kai.”

 

Gwamnan ya ƙara da cewa, yayin da aka ƙaddamar da wannan sabon shiri na shekaru biyar, akwai buƙatar kowane ɓangare ya zurfafa haɗin gwiwa, domin a tabbatar da cewa babu wanda aka bari a baya wajen gina ƙasa mai juriya da aminci.

 

A cewar sa, taken bana na “Fund Resilience, Not Disasters” ya zama wajibi a juya shi zuwa tsare-tsare na zahiri da za su tabbatar da ɗorewar kuɗaɗen da ake warewa don kula da bala’o’i, ganin cewa wannan fanni yana ta canjawa lokaci zuwa lokaci.

 

Gwamna Lawal ya kuma bayyana irin ƙalubalen da Jihar Zamfara ke fuskanta, ciki har da matsalar tsaro, gobara, ambaliyar ruwa, ruftawar ramin haƙar ma’adinai, da sauran tasirin sauyin yanayi. Duk da haka, ya yaba wa NEMA bisa kasancewa tamkar ginshiƙi wajen tallafa wa jihar a duk lokacin da ake fuskantar irin waɗannan matsaloli.

 

Ya ce, “Mun ƙarfafa hukumar mu ta Zamfara Emergency Management Agency (ZEMA) da ƙarin iko domin inganta amsawa kiran gaggawa ga bala’o’i. Muna kuma haɗa tsarin kula da haɗurra cikin tafiyar da gwamnati ta hanyar gargaɗi da wuri, haɗin kai da al’umma, da gyaran cibiyoyi — domin mu yi imani cewa juriya mai ɗorewa tana farawa daga matakin jiha.”

 

A ƙarshe, Gwamna Lawal ya miƙa godiya ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, GCFR, bisa jagorancinsa a waɗannan lokutan ƙalubale, tare da gode wa Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, GCON, da kuma Darakta Janar ta NEMA, Hajiya Zubaida Umar, bisa haɗin gwiwa da taimako da suke bai wa Zamfara don fuskantar matsalolinta.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.