• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

“Magance Hadari”? “Raba Gari Ta Fannin Tattalin Arziki Da Sin Shi Ne Hadari

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
“Magance Hadari”? “Raba Gari Ta Fannin Tattalin Arziki Da Sin Shi Ne Hadari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A baya-bayan nan, wasu cibiyoyin kasuwanci na kasashen waje a kasar Sin, sun fitar da rahotannin da ke nuna kyakkyawan fata ga kasar Sin. Misali, wani binciken da kungiyar ‘yan kasuwa ta Amurka a kasar Sin ta gudanar, ya nuna cewa, kashi 66 bisa dari na kamfanonin Amurka a kasar Sin, sun ce za su ci gaba, ko kara zuba jari a kasar Sin nan da shekaru biyu masu zuwa.

Daga watan Janairu zuwa Afrilu na wannan shekara, yawan jarin waje da kasar Sin ta yi amfani da shi, ya kai kusan yuan biliyan 500, wanda ya karu da kashi 2.2 bisa dari kan na makamancin lokaci na bara.

  • Xi Jinping Na Fatan Sin Da Janhuriyar Dimokuradiyyar Congo Za Su Yi Aiki Tare Wajen Bunkasa Ci Gaba Da Samar Da Makoma Ta Gari

A cikin shekaru uku da suka gabata, yaduwar annobar COVID-19, da rikice-rikicen yanayin siyasa na duniya, sun jefa tattalin arzikin duniya cikin koma baya. Sabanin haka, kasar Sin tana da yanayin ci gaba mai dorewa, gami da samun bunkasuwar tattalin arziki yadda ya kamata. Wannan babbar kasuwa dake da yawan al’umma sama da biliyan 1.4, da rukunin matsakaita masu kudin shiga sama da miliyan 400, ta jawo hankulan jarin waje kwarai da gaske.

Rahoton baya-bayan nan da Majalisar Dinkin Duniya ta fitar, ya daga hasashen karuwar tattalin arzikin kasar Sin a bana, daga kashi 4.8 bisa dari zuwa kashi 5.3 bisa dari.
A halin yanzu, tattalin arzikin duniya yana fuskantar wasu kalubale a fannonin bangaranci, da ra’ayin ba da kariyar ciniki.

Wasu kasashe suna ba da shawarar “Raba gari ta fannin tattalin arziki”, gami da tsara kalmar “Magance hadari” a kokarin boye yunkurinsu na murkushe kasar Sin.

Labarai Masu Nasaba

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Wani rahoton bincike daga wata cibiyar bincike ta Austriya ya yi kiyasin cewa, idan Jamus ta “raba gari” da kasar Sin, GDPn Jamus zai ragu da kashi 2 bisa dari a ko wace shekara, kwatankwacin yin asarar kudin EURO biliyan 60.

John Donahoe, babban jami’in zartaswa na kamfanin Nike, ya fada a zahiri cewa “raba gari” da kasar Sin zai zama bala’i ga kasuwancin duniya. An yi imanin cewa, kasar Sin za ta ci gaba da zama zabin farko na zuba jari, da bunkasa kasuwanci daga ‘yan kasuwar waje.
(Mai fassara: Bilkisu Xin)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

La liga Ta Zama Dandalin Masu Nuna Wariya, Cewar Vinicius

Next Post

Dalibai Sun Bukaci Tinubu Da Gwamnoni Da Su Kula Da Sha’anin Tsaro, Ilimi Da Wutar Lantarki

Related

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?
Daga Birnin Sin

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

17 hours ago
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

18 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

20 hours ago
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

20 hours ago
Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya
Daga Birnin Sin

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

22 hours ago
Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC
Daga Birnin Sin

Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC

24 hours ago
Next Post
Dalibai Sun Bukaci Tinubu Da Gwamnoni Da Su Kula Da Sha’anin Tsaro, Ilimi Da Wutar Lantarki

Dalibai Sun Bukaci Tinubu Da Gwamnoni Da Su Kula Da Sha'anin Tsaro, Ilimi Da Wutar Lantarki

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

August 27, 2025
Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

August 27, 2025
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

August 27, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

August 27, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

August 27, 2025
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

August 27, 2025
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

August 27, 2025
Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.