• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Magidanta Za Su Amfana Da Tan 42,000 Na Abinci Kyauta A Zamfara

by Leadership Hausa
1 year ago
Zamfara

Gwamna Dauda Lawal ya ƙaddamar da rabon tan 42,000 na kayan abinci daban-daban ga marasa galihu a Zamfara.

An gudanar da bikin ƙaddamarwar ne a ranar Litinin a ofishin Kwamishinan Harkokin Jinƙai na Jihar Zamfara da ke Gusau, babban birnin jihar.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa NEMA, ta miƙa wa gwamnatin jihar kayayyaki daban-daban domin rabawa ga marasa galihu.

A cewar sanarwar, Dakta Ishaya Chonoko, Daraktan Hukumar NEMA na shiyyar Arewa maso Yamma, ya wakilci Darakta Janar na Hukumar, Hajiya Zubaida Umar a wajen bikin rabon.

  • Daga Yau Litinin Zuwa Laraba Za a Ƙwalla Rana Mai Tsananin Zafi A Wasu Jihohin Nijeriya – NiMet

 

LABARAI MASU NASABA

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

A yayin jawabinsa, Gwamna Lawal ya bayyana cewa rabon kayayyakin ya zo a wani muhimmin lokaci da mutane ke fuskantar ƙalubale saboda ayyukan ’yan fashin daji da kuma tasirin manufofin da aka ɓullo da su a baya-bayan nan da nufin ƙarfafa tattalin arzikin ƙasa.

Ya ce, “Ina miƙa godiyata ga shugaban ƙasa bisa jajircewarsa na kawo ƙarshen matsalar rashin tsaro, domin idan ba tare da wannan ƙuduri ba, ba za a iya samun nasarori masu ma’ana a kowane fannin da ke taimakawa wajen cigaba ba. Babu shakka wannan taimako zai samar da agajin da ake buƙata ga waɗanda suka ci gajiyar shirin tare da bayar da goyon baya ga ƙoƙarin da gwamnatin jihar ke ci gaba da yi a wannan fanni.

Zamfara

“Wannan yunƙuri na Gwamnatin Tarayya zai haɗa da ƙoƙarin da gwamnatina ke yi na magance matsalar ’yan bindiga da ta daɗe a jihar tare da samar da tallafi ga al’ummarmu.

“Tun lokacin da na hau mulki a matsayina na gwamna, na ci gaba da yin aiki tuƙuru domin samun goyon bayan yaƙi da ’yan bindiga da tallafa wa marasa galihu a faɗin jihar nan, musamman mata da yara da kuma tsofaffi. A madadin al’ummar Zamfara nagari, ina miƙa godiyata ga Gwamnatin Tarayya bisa wannan da sauran ɗimbin tallafi da ake baiwa jihar mu.

“Ba sai an faɗa ba, waɗannan kayayyaki za su taimaka matuƙa wajen rage wahalhalun abinci da mutanenmu ke fuskanta. Don haka, ina kira ga waɗanda ke karɓar kayan da su yi amfani da su yadda ya kamata.

“Da waɗannan jawabai, ina mai farin ciki a madadin gwamnati da al’ummar jihar Zamfara, na karɓi tan 42,000 na kayayyakin abinci iri-iri tare da ƙaddamar da rabon kayayyakin ga marasa galihu mazauna jihar Zamfara.

Zamfara

“Allah Maɗaukakin Sarki ya ci gaba da baiwa dukkan ƙoƙarinmu da nasara a matakai daban-daban na gwamnati. Ya kuma dawo mana da zaman lafiya a tsakanin mutanenmu. Allah ya sa waɗannan kayayyaki su amfana sannan su samar da agajin gaggawa ga marasa galihu a faɗin jihar.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato
Manyan Labarai

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi
Labarai

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Mutum 18 Sun Mutu, 40 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kebbi 
Labarai

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

October 28, 2025
Next Post
Tawaga Ta 10 Ta ‘Yan Sandan Sin Masu Wanzar Da Zaman Lafiya Za Ta Tafi Sudan Ta Kudu 

Tawaga Ta 10 Ta ‘Yan Sandan Sin Masu Wanzar Da Zaman Lafiya Za Ta Tafi Sudan Ta Kudu 

LABARAI MASU NASABA

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Mutum 18 Sun Mutu, 40 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kebbi 

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

October 28, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
Zamfara

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.