• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Magidanta Za Su Amfana Da Tan 42,000 Na Abinci Kyauta A Zamfara

by Leadership Hausa
1 year ago
in Labarai
0
Magidanta Za Su Amfana Da Tan 42,000 Na Abinci Kyauta A Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Dauda Lawal ya ƙaddamar da rabon tan 42,000 na kayan abinci daban-daban ga marasa galihu a Zamfara.

An gudanar da bikin ƙaddamarwar ne a ranar Litinin a ofishin Kwamishinan Harkokin Jinƙai na Jihar Zamfara da ke Gusau, babban birnin jihar.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa NEMA, ta miƙa wa gwamnatin jihar kayayyaki daban-daban domin rabawa ga marasa galihu.

A cewar sanarwar, Dakta Ishaya Chonoko, Daraktan Hukumar NEMA na shiyyar Arewa maso Yamma, ya wakilci Darakta Janar na Hukumar, Hajiya Zubaida Umar a wajen bikin rabon.

  • Daga Yau Litinin Zuwa Laraba Za a Ƙwalla Rana Mai Tsananin Zafi A Wasu Jihohin Nijeriya – NiMet

 

Labarai Masu Nasaba

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

A yayin jawabinsa, Gwamna Lawal ya bayyana cewa rabon kayayyakin ya zo a wani muhimmin lokaci da mutane ke fuskantar ƙalubale saboda ayyukan ’yan fashin daji da kuma tasirin manufofin da aka ɓullo da su a baya-bayan nan da nufin ƙarfafa tattalin arzikin ƙasa.

Ya ce, “Ina miƙa godiyata ga shugaban ƙasa bisa jajircewarsa na kawo ƙarshen matsalar rashin tsaro, domin idan ba tare da wannan ƙuduri ba, ba za a iya samun nasarori masu ma’ana a kowane fannin da ke taimakawa wajen cigaba ba. Babu shakka wannan taimako zai samar da agajin da ake buƙata ga waɗanda suka ci gajiyar shirin tare da bayar da goyon baya ga ƙoƙarin da gwamnatin jihar ke ci gaba da yi a wannan fanni.

Zamfara

“Wannan yunƙuri na Gwamnatin Tarayya zai haɗa da ƙoƙarin da gwamnatina ke yi na magance matsalar ’yan bindiga da ta daɗe a jihar tare da samar da tallafi ga al’ummarmu.

“Tun lokacin da na hau mulki a matsayina na gwamna, na ci gaba da yin aiki tuƙuru domin samun goyon bayan yaƙi da ’yan bindiga da tallafa wa marasa galihu a faɗin jihar nan, musamman mata da yara da kuma tsofaffi. A madadin al’ummar Zamfara nagari, ina miƙa godiyata ga Gwamnatin Tarayya bisa wannan da sauran ɗimbin tallafi da ake baiwa jihar mu.

“Ba sai an faɗa ba, waɗannan kayayyaki za su taimaka matuƙa wajen rage wahalhalun abinci da mutanenmu ke fuskanta. Don haka, ina kira ga waɗanda ke karɓar kayan da su yi amfani da su yadda ya kamata.

“Da waɗannan jawabai, ina mai farin ciki a madadin gwamnati da al’ummar jihar Zamfara, na karɓi tan 42,000 na kayayyakin abinci iri-iri tare da ƙaddamar da rabon kayayyakin ga marasa galihu mazauna jihar Zamfara.

Zamfara

“Allah Maɗaukakin Sarki ya ci gaba da baiwa dukkan ƙoƙarinmu da nasara a matakai daban-daban na gwamnati. Ya kuma dawo mana da zaman lafiya a tsakanin mutanenmu. Allah ya sa waɗannan kayayyaki su amfana sannan su samar da agajin gaggawa ga marasa galihu a faɗin jihar.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbinciGwamna Dauda LawalMagidantaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Bude Bikin Matasan Sin Da Afirka Karo Na 8 A Beijing

Next Post

Tawaga Ta 10 Ta ‘Yan Sandan Sin Masu Wanzar Da Zaman Lafiya Za Ta Tafi Sudan Ta Kudu 

Related

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

4 hours ago
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

5 hours ago
Ganduje Ba Zai Hana Kwankwaso Shiga APC Ba
Labarai

Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki

6 hours ago
Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

9 hours ago
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

18 hours ago
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu
Labarai

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

20 hours ago
Next Post
Tawaga Ta 10 Ta ‘Yan Sandan Sin Masu Wanzar Da Zaman Lafiya Za Ta Tafi Sudan Ta Kudu 

Tawaga Ta 10 Ta ‘Yan Sandan Sin Masu Wanzar Da Zaman Lafiya Za Ta Tafi Sudan Ta Kudu 

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

June 30, 2025
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

June 30, 2025
Sin Ta Kalubalanci Kasashen Yammacin Duniya Da Su Tuna Da Laifinsu Na Mulkin Mallaka

Cikar MDD Shekara 80: Nasarorinmu Sun Kara Mana Kaimi Da Kyakkyawar Makoma A Nan Gaba

June 30, 2025
Ganduje Ba Zai Hana Kwankwaso Shiga APC Ba

Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki

June 30, 2025
Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

June 30, 2025
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

June 29, 2025
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.