ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Magidanta Za Su Amfana Da Tan 42,000 Na Abinci Kyauta A Zamfara

by Leadership Hausa
2 years ago
Zamfara

Gwamna Dauda Lawal ya ƙaddamar da rabon tan 42,000 na kayan abinci daban-daban ga marasa galihu a Zamfara.

An gudanar da bikin ƙaddamarwar ne a ranar Litinin a ofishin Kwamishinan Harkokin Jinƙai na Jihar Zamfara da ke Gusau, babban birnin jihar.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa NEMA, ta miƙa wa gwamnatin jihar kayayyaki daban-daban domin rabawa ga marasa galihu.

ADVERTISEMENT

A cewar sanarwar, Dakta Ishaya Chonoko, Daraktan Hukumar NEMA na shiyyar Arewa maso Yamma, ya wakilci Darakta Janar na Hukumar, Hajiya Zubaida Umar a wajen bikin rabon.

  • Daga Yau Litinin Zuwa Laraba Za a Ƙwalla Rana Mai Tsananin Zafi A Wasu Jihohin Nijeriya – NiMet

 

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

A yayin jawabinsa, Gwamna Lawal ya bayyana cewa rabon kayayyakin ya zo a wani muhimmin lokaci da mutane ke fuskantar ƙalubale saboda ayyukan ’yan fashin daji da kuma tasirin manufofin da aka ɓullo da su a baya-bayan nan da nufin ƙarfafa tattalin arzikin ƙasa.

Ya ce, “Ina miƙa godiyata ga shugaban ƙasa bisa jajircewarsa na kawo ƙarshen matsalar rashin tsaro, domin idan ba tare da wannan ƙuduri ba, ba za a iya samun nasarori masu ma’ana a kowane fannin da ke taimakawa wajen cigaba ba. Babu shakka wannan taimako zai samar da agajin da ake buƙata ga waɗanda suka ci gajiyar shirin tare da bayar da goyon baya ga ƙoƙarin da gwamnatin jihar ke ci gaba da yi a wannan fanni.

Zamfara

“Wannan yunƙuri na Gwamnatin Tarayya zai haɗa da ƙoƙarin da gwamnatina ke yi na magance matsalar ’yan bindiga da ta daɗe a jihar tare da samar da tallafi ga al’ummarmu.

“Tun lokacin da na hau mulki a matsayina na gwamna, na ci gaba da yin aiki tuƙuru domin samun goyon bayan yaƙi da ’yan bindiga da tallafa wa marasa galihu a faɗin jihar nan, musamman mata da yara da kuma tsofaffi. A madadin al’ummar Zamfara nagari, ina miƙa godiyata ga Gwamnatin Tarayya bisa wannan da sauran ɗimbin tallafi da ake baiwa jihar mu.

“Ba sai an faɗa ba, waɗannan kayayyaki za su taimaka matuƙa wajen rage wahalhalun abinci da mutanenmu ke fuskanta. Don haka, ina kira ga waɗanda ke karɓar kayan da su yi amfani da su yadda ya kamata.

“Da waɗannan jawabai, ina mai farin ciki a madadin gwamnati da al’ummar jihar Zamfara, na karɓi tan 42,000 na kayayyakin abinci iri-iri tare da ƙaddamar da rabon kayayyakin ga marasa galihu mazauna jihar Zamfara.

Zamfara

“Allah Maɗaukakin Sarki ya ci gaba da baiwa dukkan ƙoƙarinmu da nasara a matakai daban-daban na gwamnati. Ya kuma dawo mana da zaman lafiya a tsakanin mutanenmu. Allah ya sa waɗannan kayayyaki su amfana sannan su samar da agajin gaggawa ga marasa galihu a faɗin jihar.”

Zamfara
Leadership Hausa
+ postsBio
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    “Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati Na Shekarar 2025, Dakta Zacch Adedeji

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Tawaga Ta 10 Ta ‘Yan Sandan Sin Masu Wanzar Da Zaman Lafiya Za Ta Tafi Sudan Ta Kudu 

Tawaga Ta 10 Ta ‘Yan Sandan Sin Masu Wanzar Da Zaman Lafiya Za Ta Tafi Sudan Ta Kudu 

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.