ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Magidanta Za Su Amfana Da Tan 42,000 Na Abinci Kyauta A Zamfara

by Leadership Hausa
2 years ago
Zamfara

Gwamna Dauda Lawal ya ƙaddamar da rabon tan 42,000 na kayan abinci daban-daban ga marasa galihu a Zamfara.

An gudanar da bikin ƙaddamarwar ne a ranar Litinin a ofishin Kwamishinan Harkokin Jinƙai na Jihar Zamfara da ke Gusau, babban birnin jihar.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa NEMA, ta miƙa wa gwamnatin jihar kayayyaki daban-daban domin rabawa ga marasa galihu.

ADVERTISEMENT

A cewar sanarwar, Dakta Ishaya Chonoko, Daraktan Hukumar NEMA na shiyyar Arewa maso Yamma, ya wakilci Darakta Janar na Hukumar, Hajiya Zubaida Umar a wajen bikin rabon.

  • Daga Yau Litinin Zuwa Laraba Za a Ƙwalla Rana Mai Tsananin Zafi A Wasu Jihohin Nijeriya – NiMet

 

LABARAI MASU NASABA

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

A yayin jawabinsa, Gwamna Lawal ya bayyana cewa rabon kayayyakin ya zo a wani muhimmin lokaci da mutane ke fuskantar ƙalubale saboda ayyukan ’yan fashin daji da kuma tasirin manufofin da aka ɓullo da su a baya-bayan nan da nufin ƙarfafa tattalin arzikin ƙasa.

Ya ce, “Ina miƙa godiyata ga shugaban ƙasa bisa jajircewarsa na kawo ƙarshen matsalar rashin tsaro, domin idan ba tare da wannan ƙuduri ba, ba za a iya samun nasarori masu ma’ana a kowane fannin da ke taimakawa wajen cigaba ba. Babu shakka wannan taimako zai samar da agajin da ake buƙata ga waɗanda suka ci gajiyar shirin tare da bayar da goyon baya ga ƙoƙarin da gwamnatin jihar ke ci gaba da yi a wannan fanni.

Zamfara

“Wannan yunƙuri na Gwamnatin Tarayya zai haɗa da ƙoƙarin da gwamnatina ke yi na magance matsalar ’yan bindiga da ta daɗe a jihar tare da samar da tallafi ga al’ummarmu.

“Tun lokacin da na hau mulki a matsayina na gwamna, na ci gaba da yin aiki tuƙuru domin samun goyon bayan yaƙi da ’yan bindiga da tallafa wa marasa galihu a faɗin jihar nan, musamman mata da yara da kuma tsofaffi. A madadin al’ummar Zamfara nagari, ina miƙa godiyata ga Gwamnatin Tarayya bisa wannan da sauran ɗimbin tallafi da ake baiwa jihar mu.

“Ba sai an faɗa ba, waɗannan kayayyaki za su taimaka matuƙa wajen rage wahalhalun abinci da mutanenmu ke fuskanta. Don haka, ina kira ga waɗanda ke karɓar kayan da su yi amfani da su yadda ya kamata.

“Da waɗannan jawabai, ina mai farin ciki a madadin gwamnati da al’ummar jihar Zamfara, na karɓi tan 42,000 na kayayyakin abinci iri-iri tare da ƙaddamar da rabon kayayyakin ga marasa galihu mazauna jihar Zamfara.

Zamfara

“Allah Maɗaukakin Sarki ya ci gaba da baiwa dukkan ƙoƙarinmu da nasara a matakai daban-daban na gwamnati. Ya kuma dawo mana da zaman lafiya a tsakanin mutanenmu. Allah ya sa waɗannan kayayyaki su amfana sannan su samar da agajin gaggawa ga marasa galihu a faɗin jihar.”

Zamfara
Leadership Hausa
+ postsBio
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    “Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati Na Shekarar 2025, Dakta Zacch Adedeji

MASU ALAKA

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON
Labarai

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026
Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu
Labarai

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

July 17, 2026
Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau
Rahotonni

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Next Post
Tawaga Ta 10 Ta ‘Yan Sandan Sin Masu Wanzar Da Zaman Lafiya Za Ta Tafi Sudan Ta Kudu 

Tawaga Ta 10 Ta ‘Yan Sandan Sin Masu Wanzar Da Zaman Lafiya Za Ta Tafi Sudan Ta Kudu 

LABARAI MASU NASABA

Falalar Salatut Tasbihi

Falalar Salatut Tasbihi

July 17, 2026
A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026
Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

July 17, 2026
Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.