• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Magoya Bayan Aiyedatiwa Sun Ɓarke Da Sowa Bayan Nasara A Kotun Ƙoli

byAbubakar Sulaiman
3 weeks ago
Aiyedatiwa

Gwamnan Jihar Ondo, Hon. Lucky Aiyedatiwa, ya samu tarɓa daga ɗumbin magoya baya a dandalin Dimokuraɗiyya (Democracy Park) da ke Akure ranar Juma’a bayan kotun ƙoli ta tabbatar da nasararsa. Gwamnan ya dawo ne daga Abuja inda aka yanke hukuncin da ya tabbatar da sahihancin zaɓensa.

A yayin jawabi ga dubban jama’a, Aiyedatiwa ya gode wa Allah, da mutanen Jihar Ondo da duk masu goyon bayansa a lokacin shari’ar. Ya bayyana kotu a matsayin ginshiƙin dimokuraɗiyya, yana mai jaddada cewa adalci da gaskiya suna da matuƙar muhimmanci wajen ɗorewar mulki. Ya kuma yaba wa lauyoyinsa kan ƙwarewarsu tare da gode wa Shugaba Bola Tinubu bisa jagorancinsa.

  • Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo
  • Ƴansanda Sun Bankaɗo Maɓoyar Masu Garkuwa Da Mutane A Ondo

“Wannan nasara ba tawa ce kaɗai ba, ta kowa ce a Jihar Ondo,” in ji shi, yana mai ba da tabbacin kyakkyawan shugabanci da isar da alfanun dimokuraɗiyya ga jama’a.Aiyedatiwa

A jawabansu na taya murna, wasu daga cikin manyan baƙi sun bayyana hukuncin kotun a matsayin nasarar jama’a. Hon. Ifedayo Abegunde na hukumar NDDC ya ce hukuncin ya tabbatar da cewa “ƙuri’un jama’a ba a ɓata su ba.” Tsohon mataimakin gwamna, Alhaji Abdulazeez Oluboyo, ya ce Aiyedatiwa ya kafa tarihi da samun nasara a ƙananan hukumomi baki ɗaya, yayin da tsohuwar kwamishina, Mrs. Omowumi Ohwovoriole, ta bayyana hukuncin kotun a matsayin ƙarshen duk wata muhawara kan zaɓen 2024.

Taron ya samu halartar jiga-jigan gwamnati da jam’iyya ciki har da Mataimakin Gwamna, Dr. Olayide Adelami; da Uwargidan Gwamna, Mrs. da Oluwaseun Aiyedatiwa; da Kakakin majalisar jihar, Rt. Hon. Olamide Oladiji; da Sakataren Gwamnati, Dr. Taiwo Fasoranti; da Shugaban Ma’aikata, Prince Segun Omojuwa; da mambobin majalisar zartarwa ta jiha; da manyan jiga-jigan APC; da shugabannin ƙananan hukumomi da na LCDA da sauran fitattun mutane.

LABARAI MASU NASABA

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

AiyedatiwaAiyedatiwa

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025
Next Post
Makarantun Da Ba Ƙwararrun Malamai Za Su Rasa Zama Cibiyar Rubuta Jarrabawar NECO

Makarantun Da Ba Ƙwararrun Malamai Za Su Rasa Zama Cibiyar Rubuta Jarrabawar NECO

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version