Wasu mutum 19 daga Jihar Kano sun rasa rayukansu a wani mummunan hatsarin mota a yankin Kwanar Maciji da ke Ƙaramar Hukumar Pankshin, a Jihar Filato.
Shugaban Ƙaramar Hukumar, John Dasar, ya bayyana cewa motar ta kama da wuta ne yayin da mutanen ke kan hanyar komawa gida daga ɗaurin aure da aka yi a Ƙaramar Hukumar Barikin Ladi ranar Asabar.
- Majalisa Ta Tuhumi JAMB Kan Kashe Biliyan 2 Kan Abinci Da Maganin Sauro
- Huldar Sin Da Afirka Za Ta Zama Abin Koyi Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya Ta Daukacin Bil’adama
A cewarsa, an ceto mutum 11 ciki har da direban motar da wasu fasinjoji, amma sun ji munanan raunuka.
Sauran fasinjoji 19 sun ƙone ƙurmus har ba a iya gane su.
An garzaya da waɗanda suka tsira da ransu zuwa Babban Asibitin Pankshin, inda ake ba su kulawar gaggawa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp