• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mahangar Masana Kan Sayar Wa Matatar Dangote Danyen Mai Da Naira

by Khalid Idris Doya
10 months ago
in Labarai
0
Mahangar Masana Kan Sayar Wa Matatar Dangote Danyen Mai Da Naira
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masana a bangaren mai da iskar gas sun ce, umarnin da Shugaban kasa Bola Tinubu ya bayar a baya-bayan nan da ke umartar kamfanin samar da mai ta Nijeriya (NNPCL) da ta sayar wa matatar man Dangote danyen mai da naira ba zai kawo karshen matsalolin da matatar ke fuskanta a kowace rana ba.

Matakin na Tinubu dai na da manufar ganin an kawo karshen matsalolin da matatun mai na cikin gida ke fuskanta da kuma takun-saka da ake samu tsakanin NNPC da su kansu masu mamallakan matatun mai a cikin Nijeriya ciki har da matatar Dangote.

  • Ɓata-gari Sun Cinna Wa Sakatariyar APC Wuta Tare Da Lalata Kadarorin Gwamnati A Jigawa
  • Bata-gari Sun Cinna Wa Sabon Ofishin NCC Wuta A Kano

A watannin baya, matatar man Dangote ta ci gaba da kokawa kan matsalar samun danyen mai da sauran kalubalen da take fuskanta a Nijeriya, lamarin da ta nuna barazana ga yunkurinta na kawo sauki ga al’umman Nijeriya a bangaren mai.

Hakan ya faru ne sakamakon yadda ta tunkari kasar Amurka da Burazil domin shigo da danyen man duk kuwa da cewa Nijeriya ce kasa mafi yawan danyen mai a dukkanin kasashen Afrika.

Matatar man Dangote ta zargi kamfanonin kasashen waje da ke Nijeriya da yin zagon kasa ga lamarin samar da danyen mai garesu. Daga baya kuma kamfanin ya shiga takaddama da hukumar kula da lamarin mai ta Nijeriya (NMDPRA) kan bin ka’idoji.

Labarai Masu Nasaba

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

Hadimin shugaban kasa a bangaren yada labarai, Bayo Onaguga shi ne ya sanar da cewa, Tinubu ya umarcin kamfanin mai da yake sayar wa matatar man Dangote danyen mai a kan naira.

Onanuga ya ce an dauki matakin ne domin ganin an rage matsalar da ke akwai na musayar naira da dala.

Sa dai kuma, masana a bangaren sun nuna fargabar cewa duk da yunkurin na Tinubu, hakan ba zai kawo karshen matsalolin da matatar ke fuskanta ba.

Masanin harkokin mai, Barr. Ameh Madaki, ya yi amannar cewa umarnin Tinubu na sayar da danyen mai da naira ga matatar Dangote ba zai kawo karshen kalubalen da suke jibge ba.

Ya ce hakan ya faru ne sakamakon cewa Nijeriya ba ta da sauran ragowar danyen man da za ta iya sayar wa kowace matatar mai.

A cewarsa, danyen man Nijeriya kai tsaye ana sayarwa ne ga kwangilolin da suka fito daga wajen NNPCL kuma babu wani kari kan ganga miliyan 1.2 da kasar ke hakowa duk rana balle a yi maganar sayarwa ga wata matatar cikin gida.

Ameh ya ce, hanya daya kacal da za a samu sayar wa matatun man cikin kasar nan danyen mai shi ne, idan kasar ta kara yawan danyen man da take hakowa a kowace rana.

Kwararre a bangaren makamashi, Joseph Eleojo ya ce, “A ina ne kamfanin NNPCL zai samu danyen man da zai sayar wa Dangete da sauran matatun man cikin gida? Wannan shi ne shaidar da ya sa matatun man Nijeriya ba su aiki sama da shekaru 35.

“Matakin sayar wa matatar man Dangote danyen mai da naira, mataki ne mai muhimmanci kuma abun yawa ne, hakan zai rage wa matatun cikin gidan shan wahalar samun danyen man da za su sarrafa.

“Sai dai kar fa ‘yan Nijeriya su sa a ransu cewa farashin mai zai sauki idan har an sayar wa matatun cikin gida da danyen mai da naira.”

Kazalika, shugaban kamfanin harkokin makamashi na kasa da kasa, Dakta Diran Fawibe, ya ce, umarnin na Tinubu na sayar wa matatar mai danyen mai da naira zai taimaka sosai wajen inganta lamarin samar da mai a cikin Nijeriya.

Umarnin Shugaban Kasar Zai Ceto Wa Nijeriya Dala Biliyan 7.3 Duk Shekara – Adedeji

Babban Mashawarcin shugaban kasa kan haraji kuma shugaban hukumar tattara kudaden haraji ta kasa (FIRS), Zacch Adedeji, ya ce matakin da Nijeriya ta dauka na sayar da danyen mai a kan naira zai ceto wa Nijeriya a kalla dala biliyan 7.3 a kowace shekara.

Adedeji wanda ya shaida hakan a ranar Litinin ya yin da ke bayyana alfanun umarnin da Shugaban kasa Bola Tinubu ya bai wa kamfanin samar da mai ta kasa da cewar su sayar wa matatun cikin gida danyen mai a kan naira maimakon dala.

Ya ce a kowace wata, matakin zai taimaka wajen rage kashe kudaden waje da ya kai dala miliyan 660.

Shugaban FIRS, ya kara da cewa matakin na shugaban kasa zai rage wa Nijeriya dogara da musayar danyen mai wajen shigo da shi daga katare da kaso 30 zuwa 40 na kudaden da take kashewa.

A cewarsa, Nijeriya za ta iya tara rarar da ya kai kusan dala miliyan 7.3 da kuma rage wa kudaden da take kashewa duk wata a bangaren samar da man fetur da kusan kaso dala miliyan 660.

“A kowace wata, muna kashe kusan dala miliyan 660 wajen wadannan bangaren, sannan wannan mataki zai samar mana da rarar dala miliyan 7.92 kowace shekara,” ya shaida.

Idan za a tuna dai, Tinubu ya umarci kamfanin mai na kasa da ya dukufa wajen sayar da danyen mai ga Dangote da sauran matatun mai a kan naira maimakon dala. Yunkurin ya zo ne bayan takaddama da aka yi ta samu tsakanin matatar man Dangote da mahukuntan Nijeriya a bangaren mai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DangoteMan feturMatataNaira
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rashin Amfani Da Ilimin Taurari Ya Jefa Nijeriya Halin Da Take Ciki – Sheikh Muhajjadina

Next Post

Rahoton Zanga-zangar Yaƙi Da Fatara Da Tsadar Rayuwa A Nijeriya A Rana Ta 1

Related

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano
Labarai

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

7 hours ago
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 
Labarai

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

8 hours ago
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi
Labarai

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

9 hours ago
Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore
Ra'ayi Riga

Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

11 hours ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

13 hours ago
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

13 hours ago
Next Post
Bata-gari Sun Cinna Wa Sabon Ofishin NCC Wuta A Kano

Rahoton Zanga-zangar Yaƙi Da Fatara Da Tsadar Rayuwa A Nijeriya A Rana Ta 1

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 6, 2025
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

June 5, 2025
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

June 5, 2025
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

June 5, 2025
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

June 5, 2025
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

June 5, 2025
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.