• English
  • Business News
Sunday, July 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mahangar Masana Kan Sayar Wa Matatar Dangote Danyen Mai Da Naira

by Khalid Idris Doya
11 months ago
in Labarai
0
Mahangar Masana Kan Sayar Wa Matatar Dangote Danyen Mai Da Naira
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masana a bangaren mai da iskar gas sun ce, umarnin da Shugaban kasa Bola Tinubu ya bayar a baya-bayan nan da ke umartar kamfanin samar da mai ta Nijeriya (NNPCL) da ta sayar wa matatar man Dangote danyen mai da naira ba zai kawo karshen matsalolin da matatar ke fuskanta a kowace rana ba.

Matakin na Tinubu dai na da manufar ganin an kawo karshen matsalolin da matatun mai na cikin gida ke fuskanta da kuma takun-saka da ake samu tsakanin NNPC da su kansu masu mamallakan matatun mai a cikin Nijeriya ciki har da matatar Dangote.

  • Ɓata-gari Sun Cinna Wa Sakatariyar APC Wuta Tare Da Lalata Kadarorin Gwamnati A Jigawa
  • Bata-gari Sun Cinna Wa Sabon Ofishin NCC Wuta A Kano

A watannin baya, matatar man Dangote ta ci gaba da kokawa kan matsalar samun danyen mai da sauran kalubalen da take fuskanta a Nijeriya, lamarin da ta nuna barazana ga yunkurinta na kawo sauki ga al’umman Nijeriya a bangaren mai.

Hakan ya faru ne sakamakon yadda ta tunkari kasar Amurka da Burazil domin shigo da danyen man duk kuwa da cewa Nijeriya ce kasa mafi yawan danyen mai a dukkanin kasashen Afrika.

Matatar man Dangote ta zargi kamfanonin kasashen waje da ke Nijeriya da yin zagon kasa ga lamarin samar da danyen mai garesu. Daga baya kuma kamfanin ya shiga takaddama da hukumar kula da lamarin mai ta Nijeriya (NMDPRA) kan bin ka’idoji.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Hadimin shugaban kasa a bangaren yada labarai, Bayo Onaguga shi ne ya sanar da cewa, Tinubu ya umarcin kamfanin mai da yake sayar wa matatar man Dangote danyen mai a kan naira.

Onanuga ya ce an dauki matakin ne domin ganin an rage matsalar da ke akwai na musayar naira da dala.

Sa dai kuma, masana a bangaren sun nuna fargabar cewa duk da yunkurin na Tinubu, hakan ba zai kawo karshen matsalolin da matatar ke fuskanta ba.

Masanin harkokin mai, Barr. Ameh Madaki, ya yi amannar cewa umarnin Tinubu na sayar da danyen mai da naira ga matatar Dangote ba zai kawo karshen kalubalen da suke jibge ba.

Ya ce hakan ya faru ne sakamakon cewa Nijeriya ba ta da sauran ragowar danyen man da za ta iya sayar wa kowace matatar mai.

A cewarsa, danyen man Nijeriya kai tsaye ana sayarwa ne ga kwangilolin da suka fito daga wajen NNPCL kuma babu wani kari kan ganga miliyan 1.2 da kasar ke hakowa duk rana balle a yi maganar sayarwa ga wata matatar cikin gida.

Ameh ya ce, hanya daya kacal da za a samu sayar wa matatun man cikin kasar nan danyen mai shi ne, idan kasar ta kara yawan danyen man da take hakowa a kowace rana.

Kwararre a bangaren makamashi, Joseph Eleojo ya ce, “A ina ne kamfanin NNPCL zai samu danyen man da zai sayar wa Dangete da sauran matatun man cikin gida? Wannan shi ne shaidar da ya sa matatun man Nijeriya ba su aiki sama da shekaru 35.

“Matakin sayar wa matatar man Dangote danyen mai da naira, mataki ne mai muhimmanci kuma abun yawa ne, hakan zai rage wa matatun cikin gidan shan wahalar samun danyen man da za su sarrafa.

“Sai dai kar fa ‘yan Nijeriya su sa a ransu cewa farashin mai zai sauki idan har an sayar wa matatun cikin gida da danyen mai da naira.”

Kazalika, shugaban kamfanin harkokin makamashi na kasa da kasa, Dakta Diran Fawibe, ya ce, umarnin na Tinubu na sayar wa matatar mai danyen mai da naira zai taimaka sosai wajen inganta lamarin samar da mai a cikin Nijeriya.

Umarnin Shugaban Kasar Zai Ceto Wa Nijeriya Dala Biliyan 7.3 Duk Shekara – Adedeji

Babban Mashawarcin shugaban kasa kan haraji kuma shugaban hukumar tattara kudaden haraji ta kasa (FIRS), Zacch Adedeji, ya ce matakin da Nijeriya ta dauka na sayar da danyen mai a kan naira zai ceto wa Nijeriya a kalla dala biliyan 7.3 a kowace shekara.

Adedeji wanda ya shaida hakan a ranar Litinin ya yin da ke bayyana alfanun umarnin da Shugaban kasa Bola Tinubu ya bai wa kamfanin samar da mai ta kasa da cewar su sayar wa matatun cikin gida danyen mai a kan naira maimakon dala.

Ya ce a kowace wata, matakin zai taimaka wajen rage kashe kudaden waje da ya kai dala miliyan 660.

Shugaban FIRS, ya kara da cewa matakin na shugaban kasa zai rage wa Nijeriya dogara da musayar danyen mai wajen shigo da shi daga katare da kaso 30 zuwa 40 na kudaden da take kashewa.

A cewarsa, Nijeriya za ta iya tara rarar da ya kai kusan dala miliyan 7.3 da kuma rage wa kudaden da take kashewa duk wata a bangaren samar da man fetur da kusan kaso dala miliyan 660.

“A kowace wata, muna kashe kusan dala miliyan 660 wajen wadannan bangaren, sannan wannan mataki zai samar mana da rarar dala miliyan 7.92 kowace shekara,” ya shaida.

Idan za a tuna dai, Tinubu ya umarci kamfanin mai na kasa da ya dukufa wajen sayar da danyen mai ga Dangote da sauran matatun mai a kan naira maimakon dala. Yunkurin ya zo ne bayan takaddama da aka yi ta samu tsakanin matatar man Dangote da mahukuntan Nijeriya a bangaren mai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DangoteMan feturMatataNaira
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rashin Amfani Da Ilimin Taurari Ya Jefa Nijeriya Halin Da Take Ciki – Sheikh Muhajjadina

Next Post

Rahoton Zanga-zangar Yaƙi Da Fatara Da Tsadar Rayuwa A Nijeriya A Rana Ta 1

Related

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027
Labarai

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

8 hours ago
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC
Manyan Labarai

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

8 hours ago
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa
Labarai

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

16 hours ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

16 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

19 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

19 hours ago
Next Post
Bata-gari Sun Cinna Wa Sabon Ofishin NCC Wuta A Kano

Rahoton Zanga-zangar Yaƙi Da Fatara Da Tsadar Rayuwa A Nijeriya A Rana Ta 1

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

July 5, 2025
Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

July 5, 2025
‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

July 5, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

July 5, 2025
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

July 5, 2025
Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

July 5, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

July 5, 2025
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

July 5, 2025
Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.