ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mahangar Masana Kan Sayar Wa Matatar Dangote Danyen Mai Da Naira

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Masana

Masana a bangaren mai da iskar gas sun ce, umarnin da Shugaban kasa Bola Tinubu ya bayar a baya-bayan nan da ke umartar kamfanin samar da mai ta Nijeriya (NNPCL) da ta sayar wa matatar man Dangote danyen mai da naira ba zai kawo karshen matsalolin da matatar ke fuskanta a kowace rana ba.

Matakin na Tinubu dai na da manufar ganin an kawo karshen matsalolin da matatun mai na cikin gida ke fuskanta da kuma takun-saka da ake samu tsakanin NNPC da su kansu masu mamallakan matatun mai a cikin Nijeriya ciki har da matatar Dangote.

  • Ɓata-gari Sun Cinna Wa Sakatariyar APC Wuta Tare Da Lalata Kadarorin Gwamnati A Jigawa
  • Bata-gari Sun Cinna Wa Sabon Ofishin NCC Wuta A Kano

A watannin baya, matatar man Dangote ta ci gaba da kokawa kan matsalar samun danyen mai da sauran kalubalen da take fuskanta a Nijeriya, lamarin da ta nuna barazana ga yunkurinta na kawo sauki ga al’umman Nijeriya a bangaren mai.

ADVERTISEMENT

Hakan ya faru ne sakamakon yadda ta tunkari kasar Amurka da Burazil domin shigo da danyen man duk kuwa da cewa Nijeriya ce kasa mafi yawan danyen mai a dukkanin kasashen Afrika.

Matatar man Dangote ta zargi kamfanonin kasashen waje da ke Nijeriya da yin zagon kasa ga lamarin samar da danyen mai garesu. Daga baya kuma kamfanin ya shiga takaddama da hukumar kula da lamarin mai ta Nijeriya (NMDPRA) kan bin ka’idoji.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

Hadimin shugaban kasa a bangaren yada labarai, Bayo Onaguga shi ne ya sanar da cewa, Tinubu ya umarcin kamfanin mai da yake sayar wa matatar man Dangote danyen mai a kan naira.

Onanuga ya ce an dauki matakin ne domin ganin an rage matsalar da ke akwai na musayar naira da dala.

Sa dai kuma, masana a bangaren sun nuna fargabar cewa duk da yunkurin na Tinubu, hakan ba zai kawo karshen matsalolin da matatar ke fuskanta ba.

Masanin harkokin mai, Barr. Ameh Madaki, ya yi amannar cewa umarnin Tinubu na sayar da danyen mai da naira ga matatar Dangote ba zai kawo karshen kalubalen da suke jibge ba.

Ya ce hakan ya faru ne sakamakon cewa Nijeriya ba ta da sauran ragowar danyen man da za ta iya sayar wa kowace matatar mai.

A cewarsa, danyen man Nijeriya kai tsaye ana sayarwa ne ga kwangilolin da suka fito daga wajen NNPCL kuma babu wani kari kan ganga miliyan 1.2 da kasar ke hakowa duk rana balle a yi maganar sayarwa ga wata matatar cikin gida.

Ameh ya ce, hanya daya kacal da za a samu sayar wa matatun man cikin kasar nan danyen mai shi ne, idan kasar ta kara yawan danyen man da take hakowa a kowace rana.

Kwararre a bangaren makamashi, Joseph Eleojo ya ce, “A ina ne kamfanin NNPCL zai samu danyen man da zai sayar wa Dangete da sauran matatun man cikin gida? Wannan shi ne shaidar da ya sa matatun man Nijeriya ba su aiki sama da shekaru 35.

“Matakin sayar wa matatar man Dangote danyen mai da naira, mataki ne mai muhimmanci kuma abun yawa ne, hakan zai rage wa matatun cikin gidan shan wahalar samun danyen man da za su sarrafa.

“Sai dai kar fa ‘yan Nijeriya su sa a ransu cewa farashin mai zai sauki idan har an sayar wa matatun cikin gida da danyen mai da naira.”

Kazalika, shugaban kamfanin harkokin makamashi na kasa da kasa, Dakta Diran Fawibe, ya ce, umarnin na Tinubu na sayar wa matatar mai danyen mai da naira zai taimaka sosai wajen inganta lamarin samar da mai a cikin Nijeriya.

Umarnin Shugaban Kasar Zai Ceto Wa Nijeriya Dala Biliyan 7.3 Duk Shekara – Adedeji

Babban Mashawarcin shugaban kasa kan haraji kuma shugaban hukumar tattara kudaden haraji ta kasa (FIRS), Zacch Adedeji, ya ce matakin da Nijeriya ta dauka na sayar da danyen mai a kan naira zai ceto wa Nijeriya a kalla dala biliyan 7.3 a kowace shekara.

Adedeji wanda ya shaida hakan a ranar Litinin ya yin da ke bayyana alfanun umarnin da Shugaban kasa Bola Tinubu ya bai wa kamfanin samar da mai ta kasa da cewar su sayar wa matatun cikin gida danyen mai a kan naira maimakon dala.

Ya ce a kowace wata, matakin zai taimaka wajen rage kashe kudaden waje da ya kai dala miliyan 660.

Shugaban FIRS, ya kara da cewa matakin na shugaban kasa zai rage wa Nijeriya dogara da musayar danyen mai wajen shigo da shi daga katare da kaso 30 zuwa 40 na kudaden da take kashewa.

A cewarsa, Nijeriya za ta iya tara rarar da ya kai kusan dala miliyan 7.3 da kuma rage wa kudaden da take kashewa duk wata a bangaren samar da man fetur da kusan kaso dala miliyan 660.

“A kowace wata, muna kashe kusan dala miliyan 660 wajen wadannan bangaren, sannan wannan mataki zai samar mana da rarar dala miliyan 7.92 kowace shekara,” ya shaida.

Idan za a tuna dai, Tinubu ya umarci kamfanin mai na kasa da ya dukufa wajen sayar da danyen mai ga Dangote da sauran matatun mai a kan naira maimakon dala. Yunkurin ya zo ne bayan takaddama da aka yi ta samu tsakanin matatar man Dangote da mahukuntan Nijeriya a bangaren mai.

Masana
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Labarai

Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

July 12, 2026
NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli
Labarai

NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

July 12, 2026
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe
Labarai

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

July 12, 2026
Next Post
Bata-gari Sun Cinna Wa Sabon Ofishin NCC Wuta A Kano

Rahoton Zanga-zangar Yaƙi Da Fatara Da Tsadar Rayuwa A Nijeriya A Rana Ta 1

LABARAI MASU NASABA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

July 12, 2026
NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

July 12, 2026
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

July 12, 2026
NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

July 12, 2026
inec

2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina

July 12, 2026
Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

July 11, 2026
Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

July 11, 2026
Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

July 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.