• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mahara Sun Halaka Wasu ‘Yan Kasuwa 8 A Katsina

by Muhammad
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Jiragen NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Lalata Baburansu 40 Da Bindigu 6 A Borno
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan bindiga sun kashe wasu mutane takwas a lokacin da suka kai wani hari kan ayarin motocin ‘yan kasuwa da ke dawowa daga kasuwar garin Yantumaki da ke karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina.

Wata majiya mai tushe, wanda shugaban kungiyar direbobi a yankin, Kabiru Dangaye, ya bayyana cewa ‘yan ta’addar sun bude wuta kan ‘yan kasuwar ne a daidai lokacin da sojoji dauke da makamai suka yi wa ‘yan kasuwar rakiya cikin motoci 25 a ranar Juma’a.

  • Kisan Katsina: Mun Rasa Rayuka 102 -Shugaban Al’umma 
  • Gwamnatin Nijeriya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Da Aka Yi Wa ‘Yan Banga A Katsina

Ya ce mutane takwas ne suka mutu nan take sakamakon harin yayin da aka kai wadanda suka jikkata asibiti don kula da lafiyarsu.

Shugaban ya ce, “Direban mu sun jira sa’o’i da dama kamar yadda suka saba kafin sauran direbobi da ‘yan kasuwa su zo daga unguwannin makwabta domin fara tafiya. Muna da motoci kusan 25 daga nan sai muka kira sojoji su zo su yi mana rakiya kamar yadda muka saba, sojoji suka shiga motarsu.”

Dangaye ya kara da cewa, sun tashi daga Mai Dabino da ke yankin Danmusa, inda suka tashi a cikin ayari, inda suka wuce Sabon Garin Nasarawa da Mahuta, sai suka yi kwanton bauna a kewayen unguwar Makera.

Labarai Masu Nasaba

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

“’Yan ta’addar sun kasu kashi hudu ne kuma a lokacin da babbar motar ta isa rukuni na uku ne ‘yan ta’addar suka fara harbin. A lokacin da sojoji suke tuki a baya, da nufin tafiya gaba da sauri, sai wasu ‘yan ta’addar suka fara harbe-harbe a kansu, amma sojoji sun yi ta harbin kan mai uwa da wabi, saboda karfinsu, ‘yan ta’addar sun yi galaba a kan sojoji.” a cewarsu.

Dangaye ya kara da cewa an yi kira don a kawo dauki ga tawagar da karin sojoji domin taimakawa ‘yan kasuwar.

Har yanzu dai rundunar ‘yan sandan jihar Katsina ba ta ce uffan ba kan harin, duk da kokarin jin ta bakin mai magana da yawun ‘yan sandan jihar, Abubakar Sadik, ya ci tura har zuwa lokacin mika rahoton.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan KasuwaKatsinaMahara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Morocco Ta Kwace Tan 1.4 Na Hodar Iblis Da Aka Boye A Cikin Ayaba

Next Post

Dalibin Kasar Benin: Ina Da Burin Kai Fasahohin Aikin Noma Na Kasar Sin Zuwa Kasar Benin

Related

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

7 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

8 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

1 day ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

1 day ago
NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja
Manyan Labarai

NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

1 day ago
Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa
Manyan Labarai

Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa

2 days ago
Next Post
Dalibin Kasar Benin: Ina Da Burin Kai Fasahohin Aikin Noma Na Kasar Sin Zuwa Kasar Benin

Dalibin Kasar Benin: Ina Da Burin Kai Fasahohin Aikin Noma Na Kasar Sin Zuwa Kasar Benin

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.