• English
  • Business News
Friday, October 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mai Daki Shi Ya San Inda Yake Masa Yoyo

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Mai Daki Shi Ya San Inda Yake Masa Yoyo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasar Sin ta ce ba za ta taba tilastawa kasashen duniya koyi da dabaru ko manufinta na raya kasa ba, haka kuma ba za ta amince wata kasa ta kakaba mata nata tsari ba.

Hakika, kasar Sin ta riga ta zabi hanyarta ta raya kasa da tabbatar da tsaro da tafiyar da harkokinta na cikin gida tare kulawa da al’ummarta. Ta yi, kuma an ga irin nasarori da dimbin ci gaba da ta samu.

  • Wakilan Amurka Da Rasha Sun Tattauna Kan Batun Yakin Ukraine

Kasashe da yankuna sun bambanta, haka ma al’adu da tsaruka, kuma a tunanina, wannan shi ya sa duniyar ta zama abun sha’awa. Don haka, kamata ya yi bambancin dake tsakaninmu, ya zama hanya ta samu karin ilimi da wadata, ba wai ta nuna wariya ko danniya ba.

Kamar yadda Hausawa kan ce, mai daki, shi ya san inda yake masa yoyo, gwamnati da al’umma ne suka san karfi da arzikin da kuma rauninsu, haka kuma su ne suka san yanayi da al’adun da bukatunsu, don haka, bai dace a ce wata kasa daga waje ce za ta tsara musu dabarun raya kansu ba.

Kamar yadda mataimkain shugaban sashen wayar da kai na kwamitin kolin Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin Sun Yeli ya bayyana, a shirye kasar Sin take ta ba kasashen duniya damar koyon dabarunta idan suna sha’awa, amma ba bisa tilas ba.

Labarai Masu Nasaba

Xi Da Takwaransa Na Singapore Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 35 Da Kulla Huldar Diflomasiyya

Manyan Jami’an Kasashen Afirka Suna Fatan Fadada Hadin Gwiwa Da Kasar Sin

Ina ganin, yanzu kai ya riga ya waye, kasashe sun san tsarin da ya dace da su da kuma wadanda ba su dace, haka kuma sun san mai kaunarsu da gaske. Haka kuma kowa a duniya shaida ne na yadda kasar Sin ta gina kanta da karfin da tsari da dabarun da ta zabarwa kanta ba tare da danniya ko mulkin mallaka ko kwaikwayon wani ba.

Lokaci ya yi da ya kamata kasashen duniya su yi yaki da kokarin da kasashe masu ganin suna da karfi ke yi, na kakaba musu irin na su tsari ko yi musu danniya.

Dole ne shugabannin kasashe musammam na Afrika, su rika la’akari da yanayin da suke ciki da kuma bukatun al’ummominsu domin tsara manufofin da zai dace da su tare da ba su ikon tsaya da karfarsu ba zama ‘yan amshin shata ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sabuwar Kasar Sin Ta Ba ‘Yan Uwanta Na Nahiyar Afirka Alfahari

Next Post

Bai Kamata A Sabawa Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Ba

Related

Xi Da Takwaransa Na Singapore Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 35 Da Kulla Huldar Diflomasiyya
Daga Birnin Sin

Xi Da Takwaransa Na Singapore Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 35 Da Kulla Huldar Diflomasiyya

35 minutes ago
Manyan Jami’an Kasashen Afirka Suna Fatan Fadada Hadin Gwiwa Da Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Manyan Jami’an Kasashen Afirka Suna Fatan Fadada Hadin Gwiwa Da Kasar Sin

19 hours ago
Balaguron Fasinjoji Ta Jirgin Kasa A Kasar Sin Ya Kai Matsayi Mafi Girma A Bikin Ranar Kafuwar PRC
Daga Birnin Sin

Balaguron Fasinjoji Ta Jirgin Kasa A Kasar Sin Ya Kai Matsayi Mafi Girma A Bikin Ranar Kafuwar PRC

21 hours ago
Xi Ya Taya Jami’ar Tianjin Murnar Cika Shekaru 130 Da Kafuwa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Taya Jami’ar Tianjin Murnar Cika Shekaru 130 Da Kafuwa

23 hours ago
Kasar Sin Ta Nuna Takaici Da Matakin Amurka Na Kin Amincewa Da Daftarin Kudurin Gaza
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Nuna Takaici Da Matakin Amurka Na Kin Amincewa Da Daftarin Kudurin Gaza

1 day ago
Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Gwamnatin Amurka Ta Tsayar Da Ayyukanta
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Gwamnatin Amurka Ta Tsayar Da Ayyukanta

2 days ago
Next Post
Bai Kamata A Sabawa Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Ba

Bai Kamata A Sabawa Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Ba

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Takwaransa Na Singapore Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 35 Da Kulla Huldar Diflomasiyya

Xi Da Takwaransa Na Singapore Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 35 Da Kulla Huldar Diflomasiyya

October 3, 2025
Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin

Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin

October 3, 2025
Yadda Na Ji Bayan Faduwa Zaben 2015 – Jonathan 

Ko Jonathan Zai Iya Ja Da Tinubu A 2027?

October 3, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

October 3, 2025
NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

October 3, 2025
Goron Sallah

GORON JUMA’A

October 3, 2025
NDLEA Ta Kama Kilo 588 Na Miyagun Ƙwayoyi, Ta Ƙona Hekta 6 Na Gonakin Wiwi A Adamawa

NDLEA Ta Kama Kilo 588 Na Miyagun Ƙwayoyi, Ta Ƙona Hekta 6 Na Gonakin Wiwi A Adamawa

October 3, 2025
Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taba Yi

Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taba Yi

October 3, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

‘Yan Nijeriya Na Karbar Sakamakonsu Da Hannun Hagu A Wajen Tinubu – Atiku

October 3, 2025
Raya Al’ada: Bikin Kalankuwa Na 2025 A Kano

Raya Al’ada: Bikin Kalankuwa Na 2025 A Kano

October 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.