ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wakilan Amurka Da Rasha Sun Tattauna Kan Batun Yakin Ukraine

by Sadiq
4 years ago
Amurka

Sakatarorin tsaron Amurka da na Rasha sun tattauna ta wayar tarho, a wani yunkuri na ba kasafai ake mu’amala ba tsakanin kasashen biyu tun bayan da Rasha ta mamaye Ukraine.

Sakataren tsaron Amurka, Lloyd Austin da takwaransa na Rasha Sergei Shoigu sun gana ne a ranar Juma’a, kamar yadda kasashen biyu suka tabbatar.

  • Bukatar Kawo Karshen Rushewar Gine-gine A Nijeriya (Ra’ayinmu)
  • DA DUMI-DUMI: An Sanya Wa ‘Yan Nijeriya Dokar Hana Samun Izinin Shiga Dubai

Bangarorin biyu sun ce an tattauna ne kan halin da ake ciki a Ukraine.

ADVERTISEMENT

Wannan dai shi ne karo na farko da kasashen biyu suka bayar da bayanin wata tattaunawa tun ranar 13 ga Mayu 2022.

Bayan tattaunawar ta ranar Juma’a, ma’aikatar tsaron Amurka ta Pentagon ta ce Mista Austin “ya jaddada muhimmancin kiyaye layukan sadarwa a Ukraine”.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina

Gwamnatin Jigawa Ta Ɗaga Mafi Ƙarancin Fansho Zuwa Naira 20,000

Ma’aikatar tsaron Rasha kuwa ta ce “an tattauna batutuwan da suka shafi tsaron kasa da kasa ciki har da halin da ake ciki a Ukraine”.

Bayan tattaunawar da suka yi a baya a watan Mayu, Mista Austin ya bukaci takwaransa da ya kira tsagaita bude wuta cikin gaggawa, ko da yake Amurka ba ta ambaci bukatar ba a wannan karon.

Hakan dai na zuwa ne bayan da shugaban Kasar Rasha, Vladimir Putin ya bayyana cewa watakila a shirye yake ya yi amfani da makaman nukiliya a Ukraine, da kuma gargadin da shugaban Amurka Joe Biden ya yi.

Hukumomin Amurka da Birtaniya sun ce sun yi imanin cewa yiwuwar Mista Putin na aiwatar da wadannan barazanar babu tabbas.

Rikicin da ya yi tsami tsakanin Amurka da Rasha ya kara tabarbarewa tun bayan mamayar Ukraine.

Shugabannin kasashen biyu sun yi wata ganawa a tsakiyar shekarar 2021, wanda aka bayyana a matsayin wani mataki mai kyau na kyautata alaka.

Amma wannan ci gaban ya tsaya bayan da tashe-tashen hankula suka yi kamari a Ukraine.

Tun bayan mamayar dai babu wata tattaunawa tsakanin shugabannin kasashen Amurka da Rasha.

MASU ALAKA

Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace A Taraba
Manyan Labarai

Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina

July 8, 2026
Dole Ne Mace Ta Gaya Wa Mijinta Gaskiya Domin Ranar Hisabi – Matar Gwamnan Jigawa
Manyan Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Ɗaga Mafi Ƙarancin Fansho Zuwa Naira 20,000

July 8, 2026
Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi
Manyan Labarai

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

July 7, 2026
Next Post
Gwamnatin Jigawa Ta Hada Gwiwa Da Kasar Netherland Don Kawo Karshen Ambaliyar Ruwa 

Gwamnatin Jigawa Ta Hada Gwiwa Da Kasar Netherland Don Kawo Karshen Ambaliyar Ruwa 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Kwankwaso Ya Mayar wa Ali Modu Sheriff Martani, Ya Ce Peter Obi Na da Gagarumin Goyon Baya a Arewa

July 8, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace A Taraba

Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina

July 8, 2026
An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing

An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing

July 8, 2026
Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar

Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar

July 8, 2026
Dole Ne Mace Ta Gaya Wa Mijinta Gaskiya Domin Ranar Hisabi – Matar Gwamnan Jigawa

Gwamnatin Jigawa Ta Ɗaga Mafi Ƙarancin Fansho Zuwa Naira 20,000

July 8, 2026
Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

July 7, 2026
Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

July 7, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

July 7, 2026
Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.