ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wakilan Amurka Da Rasha Sun Tattauna Kan Batun Yakin Ukraine

by Sadiq
4 years ago
Amurka

Sakatarorin tsaron Amurka da na Rasha sun tattauna ta wayar tarho, a wani yunkuri na ba kasafai ake mu’amala ba tsakanin kasashen biyu tun bayan da Rasha ta mamaye Ukraine.

Sakataren tsaron Amurka, Lloyd Austin da takwaransa na Rasha Sergei Shoigu sun gana ne a ranar Juma’a, kamar yadda kasashen biyu suka tabbatar.

  • Bukatar Kawo Karshen Rushewar Gine-gine A Nijeriya (Ra’ayinmu)
  • DA DUMI-DUMI: An Sanya Wa ‘Yan Nijeriya Dokar Hana Samun Izinin Shiga Dubai

Bangarorin biyu sun ce an tattauna ne kan halin da ake ciki a Ukraine.

ADVERTISEMENT

Wannan dai shi ne karo na farko da kasashen biyu suka bayar da bayanin wata tattaunawa tun ranar 13 ga Mayu 2022.

Bayan tattaunawar ta ranar Juma’a, ma’aikatar tsaron Amurka ta Pentagon ta ce Mista Austin “ya jaddada muhimmancin kiyaye layukan sadarwa a Ukraine”.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ma’aikatar tsaron Rasha kuwa ta ce “an tattauna batutuwan da suka shafi tsaron kasa da kasa ciki har da halin da ake ciki a Ukraine”.

Bayan tattaunawar da suka yi a baya a watan Mayu, Mista Austin ya bukaci takwaransa da ya kira tsagaita bude wuta cikin gaggawa, ko da yake Amurka ba ta ambaci bukatar ba a wannan karon.

Hakan dai na zuwa ne bayan da shugaban Kasar Rasha, Vladimir Putin ya bayyana cewa watakila a shirye yake ya yi amfani da makaman nukiliya a Ukraine, da kuma gargadin da shugaban Amurka Joe Biden ya yi.

Hukumomin Amurka da Birtaniya sun ce sun yi imanin cewa yiwuwar Mista Putin na aiwatar da wadannan barazanar babu tabbas.

Rikicin da ya yi tsami tsakanin Amurka da Rasha ya kara tabarbarewa tun bayan mamayar Ukraine.

Shugabannin kasashen biyu sun yi wata ganawa a tsakiyar shekarar 2021, wanda aka bayyana a matsayin wani mataki mai kyau na kyautata alaka.

Amma wannan ci gaban ya tsaya bayan da tashe-tashen hankula suka yi kamari a Ukraine.

Tun bayan mamayar dai babu wata tattaunawa tsakanin shugabannin kasashen Amurka da Rasha.

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Gwamnatin Jigawa Ta Hada Gwiwa Da Kasar Netherland Don Kawo Karshen Ambaliyar Ruwa 

Gwamnatin Jigawa Ta Hada Gwiwa Da Kasar Netherland Don Kawo Karshen Ambaliyar Ruwa 

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.