• English
  • Business News
Sunday, August 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mai Dokar Barci…

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Mai Dokar Barci…
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da alamun kasashen da suke ikirarin kare hakkin bil-Adama, su ne kuma suke take wannan hakki ta hanyar kashe fararen hula, wadanda ba su san hawa ba balle sauka. Wai mai dokar barci ya bige da gyangyadi.

Sanin kowa ne cewa, a kan tura sojojin kiyaye zaman lafiya zuwa wasu kasashe dake fama da rikici ko tashe-tashen hankula ne, domin su tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin wadannan kasashe, amma sabanin haka, sai irin wadannan kasashe, har ma gasar kashe fararen hula suka yi a kasar Afghanistan.

  • Dan Ta’addar Da Aka Nada Sarauta A Zamfara Ya Kashe Mutum 100 A Katsina – ‘Yansanda

Wani binciken da kafar yada labaran BBC ta gudanar kan shaidun da suka hada da rahotannin sojojin Birtaniyya, da sakonnin imel, da hotunan ramukan harsashi a wurin, ya nuna cewa, wasu mambobin tsohon rukunin mai ba da hidima ga soja na musamman na Birtaniya dake Afghanistan, sun sha kashe fursunoni da fararen hula da ba sa dauke da makamai, har ma su kan yi gasar kisan mutane, daga cikinsu, akwai yiwuwar wata runduna ta kashe mutane har 54 ba bisa kai’da ba, a wa’adinsu na watanni 6 a wurin.

Bayan fallasa wadannan laifuffuka, ma’aikatar tsaron Burtaniya, ba wai kawai ta ki neman afuwa, ko daukar alhakin kai harin ba, amma sai ta yi kokarin yin rufa-rufa, tana mai zargin rahoton na BBC da cewa wai “labarai ne da ba su dace ba kuma wai ba daidai ba ne”. Wannan shi ne kora kunya da hauka.

Hasali ma, ba sojojin Birtaniya ne kawai suka kashe fararen hula babu gaira babu dalili ba. A watan Disamba na shekarar 2020, ma’aikatar tsaron kasar Austriliya, ta fitar da rahoton bincike game da kyamar bil-Adama da sojojinta suka yiwa fararen hula a kasar Afghanistan.

Labarai Masu Nasaba

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

A bangaren Amurka, wadda ke zama kanwa uwar gani, mamayar da aka yi a kasar Afghanistan na tsawon shekaru 20, ta yi sanadiyar rayukan ’yan kasar dubu 174, ciki har da fararen hula dubu 30. Wadannan kasashe su ne suke ikirari kare hakkin Bil Adama a ko da yaushe, to yaya za su bayyana kisan gillar da suke yiwa mutanen da ba su san hawa ba balle sauka a kasashen waje?Duniya na bukatar amsa daga gare su.

Sanin kowa ne cewa, yarjejeniyar Geneva ta bayyana karara cewa, ba daidai ba ne kisa, ko tilastawa, ko musgunawa da ma korar wadanda ke zaune lafiya, yin hakan ta ce haramun ne a lokacin yaki, kuma wadanda ba su taka rawa a yakin ba, za a mutunta su a kowane hali.

Kasashen Amurka da Birtaniya da Austriliya, dukkansu sun sa hannu kan wannan yarjejeniya, amma kuma sun rufe idanunsu, suka kuma rika keta dokokin kasa da kasa, da ma harkokinsu da suka shafi dan-Adam.

Baya ga yadda suke kashe mutanen da ba su ji ba su gani ba. Laifukan da suke aikatawa, laifi ne ga daukacin bil-Adam, don haka sun cancanci a yi musu adalci. Dole ne kasashen duniya su yi adalci ga wadanda ba su ji ba su gani ba. Domin babu ran da ya fi wani. (Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojoji Sun Sake Ceto Daya Daga Cikin ‘Yan Matan Chibok A Borno

Next Post

Kasar Sin Za Ta Tsaya Kan Manufar Bude Kofarta Ga Duniya

Related

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan
Daga Birnin Sin

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

13 hours ago
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar
Daga Birnin Sin

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

14 hours ago
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 
Daga Birnin Sin

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

15 hours ago
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika
Daga Birnin Sin

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

16 hours ago
Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150
Daga Birnin Sin

Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

17 hours ago
Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

1 day ago
Next Post
Kasar Sin Za Ta Tsaya Kan Manufar Bude Kofarta Ga Duniya

Kasar Sin Za Ta Tsaya Kan Manufar Bude Kofarta Ga Duniya

LABARAI MASU NASABA

Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

August 10, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

August 10, 2025
Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

August 10, 2025
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

August 10, 2025
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

August 9, 2025
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

August 9, 2025
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

August 9, 2025
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

August 9, 2025
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

August 9, 2025
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.