• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Maido Da Huldar Diflomasiya Tsakanin Sin Da Nauru Ya Sake Tabbatar Da Matsaya Guda Uku Da Kasashen Duniya Suka Cimma

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
nauru
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanan nan, al’ummun kasar Nauru dake tsibirin tekun Pasifik sun yi maraba da maido da huldar diflomasiya tsakanin Nauru da Sin. Kafin wannan, majalisar Nauru ta zartas da kudurin katse hulda tsakanin Nauru da yankin Taiwan na kasar Sin tare da maido da huldar diflomasiya da Sin.

Nauru ta maido da huldar diplomasiya tsakaninta da Sin ba tare da wani sharadi ba, wanda ya kasance shawarar diplomasiya da ta yanke da kanta, kuma ya sake tabbatar da cewa, ka’idar kasancewar Sin daya tak a duniya, ita ce matsayar da kasashen duniya suke dauka.

  • Sin Za Ta Gina Babbar Cibiyar Tattara Bayanan Sabbin Na’urori
  • Sin: Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza Shi Ne Abu Mafi Muhimmanci A Halin Yanzu

Sin da Nauru sun maido da huldar diplomasiya, wanda ya kori kalaman wai nuna adawa da kudurin MDD mai lamba 2758. Gwamnatin Nauru ta bayanna a cikin sanarwar da ta fitar cewa, bisa kudurin MDD mai lamba 2758, ta amince cewa, gwamnatin jamhuriyyar jama’ar Sin ita ce halaltacciyar gwamnati daya tilo dake wakiltar kasar Sin baki daya, kuma Taiwan wani yanki ne da ba za a iya raba shi da kasar Sin ba.

Wannan ya tabbatar da cewa, kudurin MDD mai lamba 2758 dake tabbatar manufar kasar Sin daya tak, kuduri ne da kasa da kasa suka amince da shi, kuma babu wanda zai iya sauya shi.

Ban da wannan, maido da huldar diplomasiya tsakanin sassan biyu, ya sa duniya ta kara fahimtar cewa, “’yancin kan Taiwan” ba zai samu nasara ba. Tun lokacin da jam’iyyar Democrat a yankin Taiwan ta hau karagar mulki a shekarar 2016, kasashen duniya fiye da 10 sun katse huldar dake tsakaninsu da hukumomin yankin Taiwan.

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Ministan kudi na kasar Tuvalu ya bayyana a yayin wata hirar da ya yi da kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa, ana sa ran kasar Tuvalu za ta duba yiwuwar daidaita huldar tsakaninta da yankin Taiwan. Matakin “kulla huldar diplomasiya ta hanyar biyan kudi” da gwamnatin yankin Taiwan ta dauka ba zai yi amfani ba, kuma tana cikin hadari sosai, idan har tana son rike kasashe guda 12 da ake kira “kasashen dake huldar diplomasiya da yankin”. (Safiyah Ma)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Daga Dajin Kajurun Kaduna ‘Yan Bindiga Ke Zuwa Su Addabe Mu – Mazauna Abuja

Next Post

Ya Kamata Sin Da Faransa Su Ba Da Jagora Wajen Yin Mu’amala A Shekaru 60 Masu Zuwa

Related

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su
Daga Birnin Sin

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

13 hours ago
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

14 hours ago
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko
Daga Birnin Sin

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

15 hours ago
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba
Daga Birnin Sin

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

16 hours ago
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai
Daga Birnin Sin

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

17 hours ago
An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya
Daga Birnin Sin

An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya

18 hours ago
Next Post
Ya Kamata Sin Da Faransa Su Ba Da Jagora Wajen Yin Mu’amala A Shekaru 60 Masu Zuwa

Ya Kamata Sin Da Faransa Su Ba Da Jagora Wajen Yin Mu’amala A Shekaru 60 Masu Zuwa

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

June 28, 2025
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

June 28, 2025
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

June 28, 2025
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

June 28, 2025
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

June 28, 2025
Hoton Tallan Taliyar Indomie

Indomie Ta Kaddamar Da Shirin Gangamin Abinci Mai Gina Jiki Na ‘Ingantaccen Abinci Domin Nasara’

June 28, 2025
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.