ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Sin Da Faransa Su Ba Da Jagora Wajen Yin Mu’amala A Shekaru 60 Masu Zuwa

by CGTN Hausa
2 years ago
faransa

Jiya Alhamis 25 ga wata ne a babban dakin wasan kwaikwayon kasar Sin da ke nan birnin Beijing, fadar mulkin kasar, aka nuna wasan kwaikwayon wake-wake mai suna Romeo da Juliet, wanda mai tsara kide-kide na kasar Faransa Charles Francois Gounod ya samar da shi. Masu fasaha na Sin da Faransa sun nuna wasan mai kayatarwa ne cikin hadin gwiwa, wasan da ya kasance kyautar musamman ta murnar cika shekaru 60 da kulla huldar jakadanci a tsakanin kasashen 2.

Yayin da kasar Sin ke mu’amala da kasashen yammacin duniya, Faransa ta sha bamban sosai, inda ta zama ta farko tsakanin manyan kasashen yammacin duniya da suka kulla huldar diplomasiyya da jamhuriyar jama’ar kasar Sin a hukumance, kana ta zama ta farko tsakanin manyan kasashen yammacin duniya da suka kyautata hulda da Sin zuwa huldar abokantaka bisa manyan tsare-tsare daga dukkan fannoni da kuma tattaunawa da Sin dangane da manyan tsare-tsare.

  • Ilimi A Dukkan Matakai A Jihar Xinjiang Ta Kasar Sin Ya Kai Kololuwar Matsayi
  • Kayan Da Aka Jigila Cikin Sauri A Sin Ya Alamta Babban Karfin Tattalin Arzikin Kasar

A yayin liyafar da aka gudanar ta murnar cika shekaru 60 da kulla huldar diplomasiyya tsakanin Sin da Faransa a daren jiya, shugabannin kasashen 2 sun gabatar da jawabai ta kafar bidiyo, inda shugaba Xi Jinping ya jaddada cewa, tarihin musamman na huldar da ke tsakanin Sin da Faransa ya samar da ruhin Sin da Faransa mai ‘yancin kai, fahimtar juna, yin hangen nesa, moriyar juna da samun nasara tare. Ya kuma gabatar da shawarwari 4 dangane da zurfafa hadin gwiwar kasashen 2 a nan gaba, wato wajibi ne Sin da Faransa su tsaya kan raya huldarsu da habaka yin mu’amalar al’adu da kara azama kan cudanyar al’umma da yin kirar raya duniya mai sassa daban daban kuma mai adalci da tsari da oda, da bunkasar tattalin arzikin duniya mai kunshe da kowa da amfanawa kowa, da kuma nacewa kan samun moriyar juna da nasara tare. Xi ya gabatar da wadannan shawarwari 4 ne domin neman kare muradun bai daya na Sin da Faransa, da kokarin kara sauke nauyi dake wuyansu tare a duniya, shawarwarin da suka tsara manufar raya huldar da ke tsakanin Sin da Faransa a shekaru 60 masu zuwa.

ADVERTISEMENT

Sin da Faransa na da kujerun din din din a kwamitin sulhu na MDD, kuma kasashe ne masu kishin zaman lafiya da kin yarda da nuna kiyayya tsakanin rukunoni, da kuma rungumar manufar cudanyar sassa daban daban. A cikin duniyar da ke fama da tashin hankali, kamata ya yi Sin da Faransa su kara hada kansu, su daidaita matsalolin tafiyar da harkokin duniya tare, su kuma taimaka wajen kwantar da kura a duniya. (Tasallah Yuan)

 

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

faransa
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

MASU ALAKA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
Daga Birnin Sin

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Next Post
Kofin Afirka 2023: Yadda Manyan Kasashe Ke Tafka Abin Kunya

Kofin Afirka 2023: Yadda Manyan Kasashe Ke Tafka Abin Kunya

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.