• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Maimakon Yaki, Afirka Da Sin Sun Zabi Zaman Lafiya

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Maimakon Yaki, Afirka Da Sin Sun Zabi Zaman Lafiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugabanni da manyan jami’ai na kasashen Afirka ta Kudu, da Masar, da Senegal, da Congo Brazaville, da Comoros, da Zambia, da Uganda a madadin sauran kasashen Afirka, sun ziyarci kasashen Ukraine da Rasha a kwanakin baya, inda suka gana da shugabannin kasashen, tare da gabatar da shawarar maido da zaman lafiya. Wannan ziyara na tare da ma’ana ta musamman.

Kamar yadda Murithi Mutiga, darekta mai kula da harkokin nahiyar Afirka na kungiyar daidaita rikicin kasa da kasa (ICG), ya fada, wannan wani aikin shiga tsakani ne da wasu kasashen dake nahiyar Afirka suka yi a hadin gwiwar gudanarwa a wajen nahiyar Afirka, wanda ba safai a kan gan shi ba. Saboda haka batun ya nuna yadda kasashen Afirka ke samar da karin tasiri a harkokin kasa da kasa.

  • A Karon Farko Matsakaicin Shigi Da Ficin Kasuwancin Kayayyaki Ta Intanet A Shekara Tsakanin Sin Da Kasashen Ketare Ya Zarce Yuan Tiriliyan 2

Sai dai a nasu bangare, kafofin watsa labaru na kasashen yamma ba su dauki wannan ziyara da muhimmanci ba, har ma sun nuna shakku kan ma’anarta. Inda kamfanin BBC na kasar Birtaniya ya yi sharhin cewa, “kamar ba a kai ziyarar a lokacin da ya dace ba, ganin yadda bangaren Kyiv take kokarin kaddamar da hare-hare” “Ko ana neman cimma wani buri da wannan ziyara ne?” Kana kamfanin AP na kasar Amurka ya ce, “Wadannan shugabannin kasashen Afirka sun kira kansu ‘tawagar neman zaman lafiya’, amma ba a ga wani sakamakon da aka cimma ba har bayan da ganawarsu da shugabannin Ukraine da Rasha ta kai karshe.”

Hakika zancen kasashen yamma bai ba ni mamaki ba. Saboda na san sun riga sun fada cikin yakin da ake yi tsakanin Ukraine da Rasha. A ganinsu, dole ne a nuna goyon baya ga Ukraine, da yin Allah wadai da kasar Rasha. Sai dai maimakon haka, kasashen Afirka sun zabi matsayi na ba ruwanmu, da kokarin neman ganin dawowar zaman lafiya.

Amma a nata bangare, kasar Sin na da matsayin iri daya da na kasashen Afirka. A ranar 24 ga watan Fabrairun bana, ma’aikatar harkokin waje ta kasar Sin ta gabatar da wata takarda don bayyana matsayin kasar Sin game da yadda za a daidaita rikicin Ukraine ta hanyar siyasa. Kana tun daga watan Mayun bana, kasar Sin ta tura wani manzon musamman don ya ziyarci Ukraine, da Poland, da Faransa, da Jamus, da hedkwatar kungiyar kasashen Turai ta EU, gami da kasar Rasha, inda ya yi kokarin lallashin bangarori daban daban don a maido da zaman lafiya.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

A ganin kasar Sin, ya kamata a lura da damuwar kowane bangare kan tsaro, da nuna goyon baya ga duk wani matakin da zai taimakawa daidaita rikici ta hanyar sulhu.

Yanzu ko da yake akwai wuya a sanya bangarori masu ruwa da tsaki su zauna a gaban teburin shawarwari, amma abun da ya fi muhimmanci shi ne a yi kokarin samar da sharadin kawo karshen rikici sannu a hankali. Idan muka yi tsokaci bisa ra’ayin kasar Sin, to, kokarin sulhuntawa da kasashen Afirka suka yi babbar gudunmowa ce dake samar da damar daidaita rikici cikin ruwan sanyi a nan gaba.

Sa’an nan, a ganina, ziyarar shugabanni da jami’ai na Afirka a wannan karo ta nuna tasirin kasashen Afirka a duniya, gami da yadda kasashen Afirka suke dogaro da kansu a fannin tsara manufofin diplomasiyya.

’Yan Afirka ba za su maimaita abun da ya faru a lokacin manyan yake-yaken duniya guda 2 ba, inda suka halarci yaki da sadaukar da rayukansu, bisa umarnin da Turawa ‘yan mulkin mallaka suka yi. Yanzu sun iya gabatar da wata manufar da ta sha bamban da ta kasashen yamma, bisa la’akari da moriyar kansu.

Ban da haka, ko kun taba tunanin mene ne dalilin da ya sa kasashe masu tasowa irinsu kasashen Afirka, da Sin, da Indonesia, da Brazil, suka fi son ganin tsagaitar bude wuta tsakanin Rasha da Ukraine? A ganina, wannan shi ne domin akwai bambanci tsakanin kasashe masu tasowa da kasashen yamma, ta fuskar bukatunsu.

Kasashen yamma sun yi takama cewa sun fi sauran kasashe samun dimokuradiyya da ’yanci, amma a hakika suna karkashin sarrafawar wata babbar kasar dake kokarin yin babakere a duniya. Bukatarsu ita ce samun cikakken ikon tabbatar da yadda ake raba moriya a duniya, don kare tsarin duniya da ya mai da kasashen yamma a matsayin cibiya. Wannan yunkuri ya sa kasashen yamma kokarin neman “abokan gaba” a duniya da kai musu hari, ba tare da tsayawa ba.

Yayin da a nasu bangare, kasashe masu tasowa sun fi bukatar tsarin duniya mai adalci, wanda ya kunshi mabambantan bangarori masu fada a ji, da wani muhalli mai zaman lafiya da karko, inda ake iya samun ci gaban kasa mai dorewa. Idan mun yi tsokaci bisa wannan ra’ayi, za mu san cewa, kasashe masu tasowa sun fi kaunar zaman lafiya. Sai dai wani lokaci ma, sauran kasashe su kan yi musu shisshigi, da tilasta musu shiga cikin yaki.

Wani abun da ya kamata su kasashen yamma su yi la’akari a kansa, shi ne, dabarar da suka dauka, ta tayar da yaki a sauran kasashe don tabbatar da tsaron kai, da lahanta moriyar sauran kasashe don kare matsayin kansu a duniya, wato raunana saura don kare moriyar kai, wannan dabara ko za ta iya dorewa? (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Dumi-Dumi: Kotun Shari’ar Musulunci Ta Tura Sheikh Idris Abdul’aziz Gidan Yari

Next Post

“Zaman Lafiya Ta Hanyar Tattaunawa” Ita Ce Kawai Mafita Ga Gabas Ta Tsakiya

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

13 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

13 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

15 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

18 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

20 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

21 hours ago
Next Post
“Zaman Lafiya Ta Hanyar Tattaunawa” Ita Ce Kawai Mafita Ga Gabas Ta Tsakiya

“Zaman Lafiya Ta Hanyar Tattaunawa” Ita Ce Kawai Mafita Ga Gabas Ta Tsakiya

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.