• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Na Fuskantar Kalubalen Amincewa Da Kasafin Naira Tiriliyan 27.5 Na 2024

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Labarai
0
Majalisa Na Fuskantar Kalubalen Amincewa Da Kasafin Naira Tiriliyan 27.5 Na 2024
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

A ranar Laraba ce, Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya gabatar da kasafin kudi na naira tiriliyan 27.5 ga gamayyar majalisun dokoki na tarayya a wani zaman a hadin gwiwa da suka yi a majalisar wakilai.

Sai dai kuma majalisun kasar suna fuskantar kalubale na amincewa da kasafin kudin kafin karshen watan Disamba.

  • An Haramta Shan Sigari A Wuraren Shakatawa Da Makarantu A Faransa
  • Ministan Wajen Sin Ya Jaddada Shawarar Kafa Kasashe 2 A Matsayin Hanyar Warware Rikicin Falasdinu Da Isra’ila

Majalisar zartarwa ta amince da kudirin kasafin kudin a wurin taronta, kamar yadda ministan kasafi da tsare-tsaren tattalin arziki, Atiku Bagudu ya shaida wa manema labarai na fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Ya ce ana tsammanin samun kudaden shiga da suka kai na naira tiriliyan 18.32.

A cewarsa kudirin na naira tiriliyan 27.5 ya karu da sama da naira tiriliyan 1.5 idan aka kwatanta da kasafin yi na bara na naira tiriliyan 26.01.

Ya kuma ce gibin kasafin kudin ya yi kasa idan aka kwatanta da na bana.

‘Yan majalisar za su yi aiki ba dare ba rana don tantance alkaluman tare da zartar da kudurin doka wajen cika burin shugaban kasa da yake sa ran fara amfani da kasafin tun daga ranar 31 ga Disamba.

Wannan ya yi daidai da manufar tsarin kasafin kudi daga watan Janairu zuwa Disamba.

Wata majiya ta ce: “Kar ku manta cewa shugaban majalisar dattawa ya sha alwashin cewa majalisar ta 10 za ta ci gaba da gudanar da tsarin kasafin kudi na watan Janairu zuwa Disamba.

“Har ila yau, kar ku manta cewa shugaban kasa ya gargadi ministoci da shugabannin ma’aikatu da hukumomi da su rika girmama kiran kwamitocin majalisar dokokin kasa a ko da yaushe.

“Lokaci ya wuce da shugabannin ma’aikatun gwamnati za su fice daga kasa don guje wa gurfana a gaban kwamitocin majalisu.

“Bayan gabatar da kasafin kudin a ranar Laraba, majalisun kasa suna da wa’adin wata daya kacal wajen tantance kasafin tare da amincewa da shi.”

Wata majiyar kuma ta ce shugaban kwamitin kasafin kudi na majalisar dattawa, Solomon Adeola ya nuna cewa zai yi wahala majalisa ta iya gudanar da wannan aiki a kan lokaci.

Majiyar ta ci gaba da cewa: “Lokacin da yake shugabancin kwamitin kudi a majalisar dattawa ta 9, ya tabbatar da cewa an amince da wasu muhimman kudirori kamar na kudade a lokacin da ya dace duk da ya yi aiki na sa’o’i 24 kafin a kammala aikin.

“Ya ce ko ma a ce shugabannin ma’aikatu su bayyana a gaban kwamitocin majalisa wajen kare kasafinsu zai dauki lokaci.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tasirin Cutar HIV A Sin Ya Yi Matukar Raguwa

Next Post

Sama Da Kamfanoni 5,600 Ne Suka Shiga Baje Kolin Sassan Motoci Na Shanghai

Related

Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

9 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

11 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

12 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

13 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

14 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

16 hours ago
Next Post
Sama Da Kamfanoni 5,600 Ne Suka Shiga Baje Kolin Sassan Motoci Na Shanghai

Sama Da Kamfanoni 5,600 Ne Suka Shiga Baje Kolin Sassan Motoci Na Shanghai

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.