ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Na Fuskantar Kalubalen Amincewa Da Kasafin Naira Tiriliyan 27.5 Na 2024

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Majalisa

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

A ranar Laraba ce, Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya gabatar da kasafin kudi na naira tiriliyan 27.5 ga gamayyar majalisun dokoki na tarayya a wani zaman a hadin gwiwa da suka yi a majalisar wakilai.

Sai dai kuma majalisun kasar suna fuskantar kalubale na amincewa da kasafin kudin kafin karshen watan Disamba.

  • An Haramta Shan Sigari A Wuraren Shakatawa Da Makarantu A Faransa
  • Ministan Wajen Sin Ya Jaddada Shawarar Kafa Kasashe 2 A Matsayin Hanyar Warware Rikicin Falasdinu Da Isra’ila

Majalisar zartarwa ta amince da kudirin kasafin kudin a wurin taronta, kamar yadda ministan kasafi da tsare-tsaren tattalin arziki, Atiku Bagudu ya shaida wa manema labarai na fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Ya ce ana tsammanin samun kudaden shiga da suka kai na naira tiriliyan 18.32.

A cewarsa kudirin na naira tiriliyan 27.5 ya karu da sama da naira tiriliyan 1.5 idan aka kwatanta da kasafin yi na bara na naira tiriliyan 26.01.

Ya kuma ce gibin kasafin kudin ya yi kasa idan aka kwatanta da na bana.

‘Yan majalisar za su yi aiki ba dare ba rana don tantance alkaluman tare da zartar da kudurin doka wajen cika burin shugaban kasa da yake sa ran fara amfani da kasafin tun daga ranar 31 ga Disamba.

Wannan ya yi daidai da manufar tsarin kasafin kudi daga watan Janairu zuwa Disamba.

Wata majiya ta ce: “Kar ku manta cewa shugaban majalisar dattawa ya sha alwashin cewa majalisar ta 10 za ta ci gaba da gudanar da tsarin kasafin kudi na watan Janairu zuwa Disamba.

“Har ila yau, kar ku manta cewa shugaban kasa ya gargadi ministoci da shugabannin ma’aikatu da hukumomi da su rika girmama kiran kwamitocin majalisar dokokin kasa a ko da yaushe.

“Lokaci ya wuce da shugabannin ma’aikatun gwamnati za su fice daga kasa don guje wa gurfana a gaban kwamitocin majalisu.

“Bayan gabatar da kasafin kudin a ranar Laraba, majalisun kasa suna da wa’adin wata daya kacal wajen tantance kasafin tare da amincewa da shi.”

Wata majiyar kuma ta ce shugaban kwamitin kasafin kudi na majalisar dattawa, Solomon Adeola ya nuna cewa zai yi wahala majalisa ta iya gudanar da wannan aiki a kan lokaci.

Majiyar ta ci gaba da cewa: “Lokacin da yake shugabancin kwamitin kudi a majalisar dattawa ta 9, ya tabbatar da cewa an amince da wasu muhimman kudirori kamar na kudade a lokacin da ya dace duk da ya yi aiki na sa’o’i 24 kafin a kammala aikin.

“Ya ce ko ma a ce shugabannin ma’aikatu su bayyana a gaban kwamitocin majalisa wajen kare kasafinsu zai dauki lokaci.”

Majalisa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Next Post
Sama Da Kamfanoni 5,600 Ne Suka Shiga Baje Kolin Sassan Motoci Na Shanghai

Sama Da Kamfanoni 5,600 Ne Suka Shiga Baje Kolin Sassan Motoci Na Shanghai

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.