• English
  • Business News
Sunday, May 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Ta Tabbatar Da Arase A Matsayin Sabon Shugaban Hukumar Kula Da ‘Yansanda

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Majalisa Ta Tabbatar Da Arase A Matsayin Sabon Shugaban Hukumar Kula Da ‘Yansanda
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwana guda da sanarwar da zabin da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi masa, Majalisar Dattawa, ta tantance tare da tabbatar da nadin tsohon Sufeto Janar na ‘yansanda, Mista Solomon Arase (Mai ritaya) a matsayin sabon shugaban hukumar kula da harkokin ‘yansanda (PSC).

 

A jiya ne Majalisar ta amince da Arase bayan tsallake tantancewar kwamitin Majalisar Dattawa kan harkokin ‘yansanda da ke karkashin jagorancin Sanata Halluru Dauda Jika (Sanatan Bauchi ta tsakiya).

  • IGP Alkali Ya Kaddamar Da Horas Da Jami’an ‘Yansanda A Borno Gabanin Zaben 2023

A lokacin da yake gabatar da rahoton aikin kwamitinsa a gaban Majalisar, Sanata Jika ya shaida cewar Arase ya cancanta ya kuma dace domin ya yi kokari sosai a lokacin da suke masa tambayoyi a yayin tantance shi, kana ya kuma tabbatar na da nagartar da zai iya jagorantar hukumar.

 

Labarai Masu Nasaba

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

Bayan gabatar da rahoton, gaba daya Majalisar ta amince da tsohon IGP din da ya zama cikakken shugaban hukumar kula da harkokin ‘yansandan Nijeriya.

 

Buhari ta cikin wasikar da ya aike wa Majalisar Dattawan a ranar Talata, da shugaban majalisar, Sanata Ahmad Lawan ya karanta a gaban kwaryar Majalisar, ya bukaci Majalisar da ta yi la’akari da zabin da ya yi wa Arase tare da tantance shi domin ya zama shugaban hukumar.

 

Buhari ya ce nadin an yi a karkashin sashi 154 (1) na kundin tsarin mulkin Nijeriya ta 1999 da aka yi wa kwaskwarima.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NDLEA Ta Kwace Kwaya Ta N1.5bn Da Cafke Mutum 1,078 Masu Safarar Kwaya A Kano.

Next Post

Ana Zargin Sojoji Da Kisan Fulani Makiyaya 39 A Nasarawa

Related

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)
Labarai

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

22 minutes ago
Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari
Labarai

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

1 hour ago
Labarai

Kungiyar Malaman Jami’o’i Ta Ba Dalibai 164 Tallafin Karatu

13 hours ago
Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)
Labarai

Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

14 hours ago
Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu
Labarai

Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

16 hours ago
Wayar Salula Na Dab Da Kai Mu Wutar Jahannama
Labarai

Wayar Salula Na Dab Da Kai Mu Wutar Jahannama

17 hours ago
Next Post
Ana Zargin Sojoji Da Kisan Fulani Makiyaya 39 A Nasarawa

Ana Zargin Sojoji Da Kisan Fulani Makiyaya 39 A Nasarawa

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

May 11, 2025
Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

May 11, 2025
Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

May 10, 2025
An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

May 10, 2025
Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

May 10, 2025

Kungiyar Malaman Jami’o’i Ta Ba Dalibai 164 Tallafin Karatu

May 10, 2025
Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

May 10, 2025
Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

May 10, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

May 10, 2025
Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

May 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.