• English
  • Business News
Wednesday, July 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dattawa Za Ta Yi Zama Na Musamman Don Karrama Buhari 

by Abubakar Sulaiman
9 hours ago
in Siyasa
0
Majalisar Dattawa Za Ta Yi Zama Na Musamman Don Karrama Buhari 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Dattawa za ta gudanar da zama na musamman a ranar Laraba, 24 ga Yuli, domin girmama tsohon shugaban ƙasa marigayi Muhammadu Buhari, wanda ya rasu a ranar 13 ga Yuli yana da shekaru 82.

A cikin wannan zama, majalisar za ta yi nazari kan rawar da Buhari ya taka wajen bunƙasa ƙasa da kuma irin gadon da ya bari a tarihin siyasar Nijeriya.

  • An Sanya Wa Titin Shendam Sunan Marigayi Muhammadu Buhari
  • Ban Tsani Buhari Ba, Ina Sukar Sa Ne Kawai Kan Matsalar Tsaro – Ortom

Wannan na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan Majalisar Zartarwa ta Ƙasa (FEC) ta gudanar da irin wannan zama na girmamawa a ranar Alhamis da ta gabata, inda Shugaba Bola Tinubu ya yaba da salon shugabancinsa.

Marigayi Buhari, ɗan asalin Daura a Jihar Katsina, ya rasu a birnin Landan kuma an binne shi a garinsu ranar 15 ga Yuli, 2025, a wata jana’iza da manyan baki daga ciki da wajen ƙasa suka halarta. Yayi mulkin Nijeriya – daga 1983 zuwa 1985 a matsayin shugaban Soja, sannan daga 2015 zuwa 2023 a matsayin shugaban da aka zaɓa ta dimokuraɗiyya.

A wani ɓangare na zaman majalisar ranar Talata, shugaban majalisar, Sanata Godswill Akpabio, ya ƙaryata jita-jitar da ke yawo cewa an amince da ƙirƙirar sabbin jihohi, yana mai cewa har yanzu babu wani ƙudurin da ya kai matakin amincewa.

Labarai Masu Nasaba

Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AkpabioBuharimajalisaSenate
ShareTweetSendShare
Previous Post

Natasha Ta Koma Majalisar Dattawa Duk Da Tsaurara Tsaro

Next Post

Sin Da Masar Za Su Karfafa Dangantakarsu Karkashin Kungiyar SCO

Related

Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100
Manyan Labarai

Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

4 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

17 hours ago
Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
Manyan Labarai

Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

18 hours ago
Mutumin El-Rufai, Baloni, Ya Fice Daga APC A Kaduna
Siyasa

Mutumin El-Rufai, Baloni, Ya Fice Daga APC A Kaduna

1 day ago
‘Yansanda Sun Hana Gudanar Da Taron Tunawa Da Ranar Haihuwar Obi A Kaduna
Labarai

‘Yansanda Sun Hana Gudanar Da Taron Tunawa Da Ranar Haihuwar Obi A Kaduna

4 days ago
Ko Kaɗan Bamu Ji Takaicin Ficewar Atiku Daga Jam’iyyar PDP Ba — Damagum
Labarai

Ko Kaɗan Bamu Ji Takaicin Ficewar Atiku Daga Jam’iyyar PDP Ba — Damagum

4 days ago
Next Post
Sin Da Masar Za Su Karfafa Dangantakarsu Karkashin Kungiyar SCO

Sin Da Masar Za Su Karfafa Dangantakarsu Karkashin Kungiyar SCO

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso  Ne Kaɗai Ɗan Siyasar Da Zai Iya Maye Gurbin Buhari — Jigo A NNPP

Kwankwaso  Ne Kaɗai Ɗan Siyasar Da Zai Iya Maye Gurbin Buhari — Jigo A NNPP

July 22, 2025
Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar

Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar

July 22, 2025
Hana Natasha Zaman Majalisa Barazana Ne Ga Dimokuraɗiyya — CLO

Hana Natasha Zaman Majalisa Barazana Ne Ga Dimokuraɗiyya — CLO

July 22, 2025
Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu

Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu

July 22, 2025
Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

July 22, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Shawarwari Da Tattaunawa

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Shawarwari Da Tattaunawa

July 22, 2025
Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaddamar Da Kwaskwarimar Majalisar Dokoki Kan Naira Biliyan 7

Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaddamar Da Kwaskwarimar Majalisar Dokoki Kan Naira Biliyan 7

July 22, 2025
Kasar Sin Tana Da Dokoki Da Ka’idoji Sama Da 180 Dake Kare Nakasassu

Kasar Sin Tana Da Dokoki Da Ka’idoji Sama Da 180 Dake Kare Nakasassu

July 22, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu

July 22, 2025
Karin Maganar Sinawa: Koyar Da Su Ya Fi Bayar Da Kifi

Karin Maganar Sinawa: Koyar Da Su Ya Fi Bayar Da Kifi

July 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.