Majalisar Wakilai ta yi watsi da kudirin da ke neman yi wa kundin tsarin mulkin kasa kwaskwarima na shekarar 1999 domin ba da damar karbar ofisoshin shugaban kasa da mataimakinsa a tsakanin shiyyoyi shida na siyasar ƙasar.
Kudirin dokar wanda mataimakin kakakin majalisar, Benjamin Okezie Kalu ya gabatar mai taken: “Kudirin dokar sauya kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya, Cap. C23, Dokokin Tarayyar Nijeriya, 2004 don samar da ka’idar karba-karba na ofisoshin shugaban kasa da mataimakin shugaban kasa na Tarayyar Nijeriya, yankin Arewa maso Yamma, yankin Arewa maso Gabas, da yankin Arewa maso Gabas, yankin Arewa ta Tsakiya. Gabas, Kudu maso Kudu, da Kudu maso Yamma da kuma Abubuwan da suka danganci (HB. 2291).
- Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025
- Majalisar Dattawa Ta Kafa Kwamitin Sa Ido Kan Gwamnatin Riƙo A Ribas
Daily Trust ta ruwaito cewa, kudirin na daga cikin kudurori bakwai na gyaran kundin tsarin mulkin kasar da aka jera don yin karatu na biyu kan takardar odar majalisar na ranar Talata.
Da yake bayar da gudunmuwa, dan majalisar wakilai Aliyu Madaki (NNPP, Kano), ya nuna adawa da kudurin, yana mai cewa, batun da kudurin ke kokarin magancewa ya yi daidai da tsarin mulkin kasa a karkashin tsarin tarayya.
Madaki ya yi nuni da cewa, ya kamata a bar wa jam’iyyun siyasa su yanke shawara kan batun na shugaban kasa, yana mai cewa babu bukatar a sanya irin wannan tanadi a cikin kundin tsarin mulkin kasa.
Sai dai dan majalisar wakilai Ali Isah na (PDP, Gombe), bai amince da matsayin Madaki ba. Ya ce sanya shugaban kasa na a tsarin karba-karba a cikin kundin tsarin mulkin kasar zai samar da adalci da sanin ya kamata ga dukkan shiyyoyin siyasar kasar nan.
Dan majalisa Sada Soli na (APC, Katsina), yayin da yake adawa da kudurin, ya ce dokar da aka gabatar “Na da illa sosai ga hadin kan kasa.”
Ya ce sanya ka’idar shugabancin karba-karba a cikin kundin tsarin mulkin kasar zai kai ga samar da abubuwa bisa cancanta.
“Hakan zai iya sanya muradun yanki da na kabilanci a gaba su zamo mafi cancanta. Zai karfafin zabin mutanen da za su iya tsayawa takara kuma zai kara kwarin gwiwa wajen fafatawa a yankin da ake samun karancin hadin kai,” in ji Soli.
Sai dai Kalu yayin da yake mayar da martani ga matsayin Soli, ya yi watsi da muhawarar da ake tafkawa a kan neman karagar mulkin, inda ya kara da cewa duk yankin siyasar kasar nan na da kwararrun mutane da za su iya samu nasarar shiga fadar shugaban kasa da mataimakinsa.
Ya ce, jigon kudirin dokar shi ne a tabbatar da cewa kowane bangare na kasar nan ya samu damar bayar da gudunmawa wajen gudanar da mulki da ci gaban kasa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp