Gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde, ya amince da biyan Naira 80,000 a matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan jihar.
Wannan na zuwa ne bayan da wata kwamitin gwamnati da wakilan kungiyar kwadago suka bayar da shawara kan karin albashin.
- Mene Ne CIIE Ke Kawowa Kamfanonin Kasashen Waje?
- Yaya Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Jagoraci Zamanantarwar Kasashe Masu Tasowa?
Sabon tsarin albashin zai fara aiki bayan kammala gyare-gyare.
A cewar Kwamishinan Yada Labarun Jihar, Prince Dotun Oyelade, Hukumar Kididdiga ta Kasa (NBS), ta bayyana Jihar Oyo a matsayin mafi kyawun yanayi ga ma’aikata a kudancin Nijeriya.
Hakan ya biyo bayan karuwar ayyukan yi da biyan albashi da gwamnan ke yi a kan lokaci.
Tun shigarsa ofis, Gwamna Makinde yana biyan albashi a kan lokaci, ya kuma kirkiro da kara jin dadin ma’aikata don rage radadin cire tallafin fetur.
Sannan ya biya tsofaffin hakkokin ‘yan fansho da wadanda suka yi ritaya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp