• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Malamai Sun Gargadi Tinubu Kan Daukar Matakin Soji A Kan Nijar

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Malamai Sun Gargadi Tinubu Kan Daukar Matakin Soji A Kan Nijar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Zauren Malaman Nijeriya ya gargadi shugaban Nijeriya kuma shugaban kungiyar ECOWAS, Bola Ahmed Tinubu dangane da yunkurin daukar matakin soji a kan Jamhuriyar Nijar, biyo bayan hambarar da gwamnatin farar hula da sojoji suka yi.

Malaman sun ce matakin ba zai haifar da sakamako mai kyau ga kasashen biyu ba.

  • An Gurfanar Da Wani Mutum Da Ya Kashe Kaninsa Dan Shekara 6
  • Nijar Ta Yanke Hulda Tsakaninta Da Nijeriya

Malaman sun nemi kowane bangare da ya dauki matakin salama cikin yanayin diflomasiyya domin tallafawa Jamhuriyar Nijar da mutanenta.

Wannan na zuwa ne bayan wata ganawa da kungiyar ta yi, inda shugabanta Aminu Inuwa Muhammad, da sakatarenta Injiniya Basheer Adamu Aliyu da suka cimma a ranar Juma’a.

Sun yi fatan cewa majalisar dokokin Nijeriya ba za ta amince wajen bari a shiga cikin wannan rigimar ba wadda ka iya zama yaki.

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Kazalika, malaman sun jawo hankalin malamai a dukkanin matakai da su dukufa wajen fadakarwa da jan hankali kan illar janyo fada tsakanin makwabta tare da tabbatar da dorewar alakar tsakanin Nijeriya da Nijar.

“Yana da kyau gwamnatin Nijeriya ta sake yin duba kan kokarin da ta ke yi, sannan kuma ga barazanar tsaro ta ko ina, wadanda su ke ta tatse ‘yar lalitar kasar, kada a afka mu cikin wani rikici da za mu iya kaucewa, kawai don mu farantawa wasu kasashen duniya a siyasance.”

Malaman da suka sanya hannu kan takardar a yayin zaman sun kai 25 daga sassa daban-daban na kasar nan, inda suka yi fatan cewa barazanar da ake gani a zahirance ba zai kai ga janyo barakar zaman lafiya a tsakanin Nijeriya da Nijar ba.

Zauren ya jadadda goyon bayan matakan diflomasiyya da a ka fara dauka ta hanyar aikewa da wakilai domin zama da jagororin sojin juyin mulkin Nijar don tattaunawa cikin salama.

“Juyin mulkin da aka yi a Jamhuriyar Nijar da ma duk wadanda a ka yi a sauran kasashen yankin SAHEL abun takaici ne, kuma ya cancanci duk masu ra’ayin dimokuradiyya su yi tir da shi da ma duk masu neman zaman lafiya a duniya.

“Duk da cewa mutane da dama na fifita dimokradiyya da tsare-tsarenta, amma hanyar samar da shugabanci na gari, abu ne da ya kebanci mutanen kowace kasa su kadai. Don haka damar mutanen Jamhuriyyar Nijar ce su bi duk hanyoyin da su ka ga sun dace domin dawo da dimokradiyya a kasarsu, idan sun ga hakan ya dace; kuma duk wani kokarin da wani zai yi, a ko ina yake, matukar ba mutanen Nijar ba, abu ne da zai yi karan tsaye ga dimokradiyya da sunan samar da dimokradiyya.”

Malaman sun ce wa’adin kwanaki bakwai da ECOWAS ta bai wa jagororin sojin kasar ya ci karo da tanade-tanaden dimokradiyya kuma shisshigi ne ga ‘yancin gudanar da kasa mai cin gashin kanta.

Sanarwar ta ce, kaso mafi rinjaye na al’ummar Nijeriya ba su goyon bayan yakar Nijar wadda ke da kyakkyawar alaka.

“Abin da ya fi wannan hatsari kuma, shiga wannan yaki zai jawo a mayar da wanan yankin namu wani zakaran gwajin dafi da za a yi amfani da shi wajen wasa kwanji da gwajin makamai, daga kasashen waje da ke da muggan manofofi ga wannan yankin.

“Kuma amfani da karfin soji zai haifar da wuce gona da iri game da babban aikin ECOWAS na samar da tsaro da kariya daga kasashen waje, ya ba da dama ga wasu su sa muke fada da juna.”

Malaman da suka sanya hannu a sanarwar sun hada da Malam Aminu Inuwa Muhammad, Jagora, Kano; Prof. Mansur Ibrahim Sokoto mni, Mamba, Sokoto; Dr. Bashir Aliyu Umar, Mamba, Kano 04 Dr. Sa’id Ahmad Dukawa, Mamba, Kano; Dr. Abubakar Muhammad Sani B/Kudu, Mamba, Jigawa; Dr. Khalid Abubakar Aliyu, Mamba, Kaduna; Prof. Muhammad Babangida Muhammad, Mamba, Kano; Prof. Salisu Shehu, Mamba, Bauchi; Prof. Ahmad Bello Dogarawa, Mamba, Kaduna; da kuma Mal Ahmad Bello Abu Maimounah, Mamba, Katsina.

Sauran su ne: Dr. Muhammad Alhaji Abubakar, Mamba, Borno; Malam Muhammad Lawal Maidoki, Sadaukin Sokoto, Mamba, Sokoto; Malam Aminu Aliyu Gusau, Modibbon Gusau, Mamba, Zamfara; Mal Shehu Muhammad Maishanu, Mamba, Zamfara; Prof Muhammad Amin Al-Amin, Mamba, Katsina; Barrister Ibrahim Muhammad Attahir, Mamba, Gombe; Dr. Salisu Ismail, Mamba, Jigawa

Dr. Abubakar Saidu, Mamba, Gombe; Engr. Ahmad Y. M. Jumba, Mamba, Bauchi; Amir Abdullahi Abubakar Lamido, Mamba, Gombe.

Kazalika akwai Dr. Ibrahim Adam Omar Disina, Mamba, Bauchi; Prof. Ahmad Murtala, Mamba, Kano; Prof. Usman M. Shuaibu Zunnurain, Mamba, Katsina; Malam Ibrahim Ado-Kurawa, Mamba, Kano da Engr. Basheer Adamu Aliyu, Sakatare, Kano.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ECOWASJuyin MulkiMalamaiNijarNijeriyaSojojiUlamaYaki
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Gurfanar Da Wani Mutum Da Ya Kashe Kaninsa Dan Shekara 6

Next Post

Na Fi So Na Fito A Masifaffiya -Amina Miloniya

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

3 hours ago
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

3 hours ago
gaza
Labarai

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

5 hours ago
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

6 hours ago
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
Labarai

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

7 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

8 hours ago
Next Post
Na Fi So Na Fito A Masifaffiya -Amina Miloniya

Na Fi So Na Fito A Masifaffiya -Amina Miloniya

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.