• English
  • Business News
Tuesday, October 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Malamai Sun Gargadi Tinubu Kan Daukar Matakin Soji A Kan Nijar

byKhalid Idris Doya
2 years ago
inLabarai
0
Malamai Sun Gargadi Tinubu Kan Daukar Matakin Soji A Kan Nijar

Zauren Malaman Nijeriya ya gargadi shugaban Nijeriya kuma shugaban kungiyar ECOWAS, Bola Ahmed Tinubu dangane da yunkurin daukar matakin soji a kan Jamhuriyar Nijar, biyo bayan hambarar da gwamnatin farar hula da sojoji suka yi.

Malaman sun ce matakin ba zai haifar da sakamako mai kyau ga kasashen biyu ba.

  • An Gurfanar Da Wani Mutum Da Ya Kashe Kaninsa Dan Shekara 6
  • Nijar Ta Yanke Hulda Tsakaninta Da Nijeriya

Malaman sun nemi kowane bangare da ya dauki matakin salama cikin yanayin diflomasiyya domin tallafawa Jamhuriyar Nijar da mutanenta.

Wannan na zuwa ne bayan wata ganawa da kungiyar ta yi, inda shugabanta Aminu Inuwa Muhammad, da sakatarenta Injiniya Basheer Adamu Aliyu da suka cimma a ranar Juma’a.

Sun yi fatan cewa majalisar dokokin Nijeriya ba za ta amince wajen bari a shiga cikin wannan rigimar ba wadda ka iya zama yaki.

Labarai Masu Nasaba

Majalisar Wakilai Ta Kafa Kwamiti Da Zai Binciki Harkokin Kirifto Da POS A Nijeriya

Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa

Kazalika, malaman sun jawo hankalin malamai a dukkanin matakai da su dukufa wajen fadakarwa da jan hankali kan illar janyo fada tsakanin makwabta tare da tabbatar da dorewar alakar tsakanin Nijeriya da Nijar.

“Yana da kyau gwamnatin Nijeriya ta sake yin duba kan kokarin da ta ke yi, sannan kuma ga barazanar tsaro ta ko ina, wadanda su ke ta tatse ‘yar lalitar kasar, kada a afka mu cikin wani rikici da za mu iya kaucewa, kawai don mu farantawa wasu kasashen duniya a siyasance.”

Malaman da suka sanya hannu kan takardar a yayin zaman sun kai 25 daga sassa daban-daban na kasar nan, inda suka yi fatan cewa barazanar da ake gani a zahirance ba zai kai ga janyo barakar zaman lafiya a tsakanin Nijeriya da Nijar ba.

Zauren ya jadadda goyon bayan matakan diflomasiyya da a ka fara dauka ta hanyar aikewa da wakilai domin zama da jagororin sojin juyin mulkin Nijar don tattaunawa cikin salama.

“Juyin mulkin da aka yi a Jamhuriyar Nijar da ma duk wadanda a ka yi a sauran kasashen yankin SAHEL abun takaici ne, kuma ya cancanci duk masu ra’ayin dimokuradiyya su yi tir da shi da ma duk masu neman zaman lafiya a duniya.

“Duk da cewa mutane da dama na fifita dimokradiyya da tsare-tsarenta, amma hanyar samar da shugabanci na gari, abu ne da ya kebanci mutanen kowace kasa su kadai. Don haka damar mutanen Jamhuriyyar Nijar ce su bi duk hanyoyin da su ka ga sun dace domin dawo da dimokradiyya a kasarsu, idan sun ga hakan ya dace; kuma duk wani kokarin da wani zai yi, a ko ina yake, matukar ba mutanen Nijar ba, abu ne da zai yi karan tsaye ga dimokradiyya da sunan samar da dimokradiyya.”

Malaman sun ce wa’adin kwanaki bakwai da ECOWAS ta bai wa jagororin sojin kasar ya ci karo da tanade-tanaden dimokradiyya kuma shisshigi ne ga ‘yancin gudanar da kasa mai cin gashin kanta.

Sanarwar ta ce, kaso mafi rinjaye na al’ummar Nijeriya ba su goyon bayan yakar Nijar wadda ke da kyakkyawar alaka.

“Abin da ya fi wannan hatsari kuma, shiga wannan yaki zai jawo a mayar da wanan yankin namu wani zakaran gwajin dafi da za a yi amfani da shi wajen wasa kwanji da gwajin makamai, daga kasashen waje da ke da muggan manofofi ga wannan yankin.

“Kuma amfani da karfin soji zai haifar da wuce gona da iri game da babban aikin ECOWAS na samar da tsaro da kariya daga kasashen waje, ya ba da dama ga wasu su sa muke fada da juna.”

Malaman da suka sanya hannu a sanarwar sun hada da Malam Aminu Inuwa Muhammad, Jagora, Kano; Prof. Mansur Ibrahim Sokoto mni, Mamba, Sokoto; Dr. Bashir Aliyu Umar, Mamba, Kano 04 Dr. Sa’id Ahmad Dukawa, Mamba, Kano; Dr. Abubakar Muhammad Sani B/Kudu, Mamba, Jigawa; Dr. Khalid Abubakar Aliyu, Mamba, Kaduna; Prof. Muhammad Babangida Muhammad, Mamba, Kano; Prof. Salisu Shehu, Mamba, Bauchi; Prof. Ahmad Bello Dogarawa, Mamba, Kaduna; da kuma Mal Ahmad Bello Abu Maimounah, Mamba, Katsina.

Sauran su ne: Dr. Muhammad Alhaji Abubakar, Mamba, Borno; Malam Muhammad Lawal Maidoki, Sadaukin Sokoto, Mamba, Sokoto; Malam Aminu Aliyu Gusau, Modibbon Gusau, Mamba, Zamfara; Mal Shehu Muhammad Maishanu, Mamba, Zamfara; Prof Muhammad Amin Al-Amin, Mamba, Katsina; Barrister Ibrahim Muhammad Attahir, Mamba, Gombe; Dr. Salisu Ismail, Mamba, Jigawa

Dr. Abubakar Saidu, Mamba, Gombe; Engr. Ahmad Y. M. Jumba, Mamba, Bauchi; Amir Abdullahi Abubakar Lamido, Mamba, Gombe.

Kazalika akwai Dr. Ibrahim Adam Omar Disina, Mamba, Bauchi; Prof. Ahmad Murtala, Mamba, Kano; Prof. Usman M. Shuaibu Zunnurain, Mamba, Katsina; Malam Ibrahim Ado-Kurawa, Mamba, Kano da Engr. Basheer Adamu Aliyu, Sakatare, Kano.

Tags: ECOWASJuyin MulkiMalamaiNijarNijeriyaSojojiUlamaYaki
ShareTweetSendShare
Khalid Idris Doya

Khalid Idris Doya

Related

Majalisar Wakilai Ta Kafa Kwamiti Da Zai Binciki Harkokin Kirifto Da POS A Nijeriya
Labarai

Majalisar Wakilai Ta Kafa Kwamiti Da Zai Binciki Harkokin Kirifto Da POS A Nijeriya

19 minutes ago
Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa
Manyan Labarai

Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa

1 hour ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Rage Kuɗin Aikin Hajjin 2026

2 hours ago
Next Post
Na Fi So Na Fito A Masifaffiya -Amina Miloniya

Na Fi So Na Fito A Masifaffiya -Amina Miloniya

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Wakilai Ta Kafa Kwamiti Da Zai Binciki Harkokin Kirifto Da POS A Nijeriya

Majalisar Wakilai Ta Kafa Kwamiti Da Zai Binciki Harkokin Kirifto Da POS A Nijeriya

October 7, 2025
Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa

Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa

October 7, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Rage Kuɗin Aikin Hajjin 2026

October 7, 2025
Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

October 6, 2025
Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 

Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 

October 6, 2025
Habakar Yin Sayayya A Lokacin Hutu Ta Nuna Kirkira Da Irin Ci Gaban Da Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samu   

Habakar Yin Sayayya A Lokacin Hutu Ta Nuna Kirkira Da Irin Ci Gaban Da Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samu   

October 6, 2025
Karamin Ofishin Jakadancin Sin Da Ke Legas Ya Yi Bikin Bunkasa Al’adu Na Bikin Tsakiyar Kaka

Karamin Ofishin Jakadancin Sin Da Ke Legas Ya Yi Bikin Bunkasa Al’adu Na Bikin Tsakiyar Kaka

October 6, 2025
Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

October 6, 2025
Nazari Ya Gano Falalen Dutse Na Yanki Mai Nisa A Duniyar Wata Ya Fi Tsananin Sanyi Fiye Da Na Yanki Na Kusa

Nazari Ya Gano Falalen Dutse Na Yanki Mai Nisa A Duniyar Wata Ya Fi Tsananin Sanyi Fiye Da Na Yanki Na Kusa

October 6, 2025
Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni

Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni

October 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.