• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Malaman Musulunci Suna Taro A Makkah Kan Ƙarfafa Samar Da Haɗin Kai A Tsakanin Musulmi

by Muhammad
2 years ago
Musulunci

A ranar Litinin dinnan aka fara gabatar da wani taron kasa da kasa mai taken “Gina Gada tsakanin Mazhabobin Musulunci da Kungiyoyin Musulunci” a birnin Makkah na kasar Saudaiyya.

Taron wanda kungiyar kasashen musulmi ta duniya MWL ta shirya kuma Sarki Salman bin Abdulaziz ya dauki nauyin taron, ya samu halartar wakilai da dama na mabiya addinin Islama. Malamai sun bayyana aniyarsu ta inganta al’amura gama gari don farfado da gudummawar da al’ummar Musulmi ke bayarwa wajen wayar da kai da samar da ci gaba.

  • Sakamakon Taron Kasashen Musulmi Da Larabawa: Saudiyya Da Nijeriya Za Su Jagoranci ‘Yantar Da Falasdin
  • Samar Da Jami’ar Musulunci A Jihar Kaduna Alheri Ne – Bola Ige

Shugaban kungiyar MWL, Mohammed Al-Issa l, ya sanar da shirin kaddamar da daftarin aiki da ke bayyana muhimman ka’idojin samar da hadin kai a tsakanin kungiyoyin Musulunci don tunkarar kalubale yadda ya kamata.

Al-Issa ya kuma bayyana irin farin cikinsa da karbar bakuncin taron mai dimbin tarihi a Makkah tare da jaddada bukatar hadin kan al’ummar Musulmi.

Al-Issa ya yi gargadi game da kalaman bangaranci, ya kuma yi kira da a rika yada labaran da suka dace a kafafen yada labarai da ke kara samar da hadin kai. Daga nan sai ya mika godiyarsa ga mahukuntan kasar Saudiyya kan goyon bayan da suke ba shi, ya kuma yi addu’ar Allah ya kara masa lafiya.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

An fara taron ya samu kyakkyawar tarba daga babban Mufti na Saudiyya, Sheikh Abdulaziz Al-Sheikh, wanda Dr. Fahd Al-Majid ya gabatar.

Al-Sheikh ya jaddada muhimmancin hadin kai a Musulunci, ya kuma yi gargadi kan illar rarrabuwar kawuna tare da bayyana irin rawar da malamai ke takawa wajen samar da hadin kai a tsakanin musulmi.

Ya godewa mai kula da masallatai masu alfarma guda biyu, Sarki Salman bin Abdulaziz kan goyon bayan taron tare da yabawa kokarin hadin kan musulmi, karkashin jagorancin Yarima Mohammed bin Salman, Yarima mai jiran gado kuma Firayim Ministan Saudiyya.

An mika godiya ga wadanda suka shirya taron, wanda MWL ya wakilta, saboda hidimar da suke ci gaba da yi wa Musulunci da Musulmai.

Hissein Brahim Taha, babban sakataren kungiyar hadin kan kasashen musulmi OIC, ya yabawa sarki Salman da yarima mai jiran gado Mohammed bisa goyon bayan taron.

Ya yi bayani cewa muhimmin taron zai inganta hadin kai a tsakanin mazhabobin Musulunci, tare da shawarwarin da za a yi amfani da su wajen samar da hadin kai da magance sabani.

Taha ya kuma yabawa kungiyar MWL bisa sadaukarwar da take yi wa Musulunci da Musulmin duniya.

A gefe guda kuma, an sanya hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna tsakanin MWL da OIC kan hadin kai a tsakanin Kungiyoyin biyu.

An rattaba hannu kan wata yarjejeniya tsakanin Cibiyar Fiqhu ta Musulunci ta MWL da Cibiyar Nazarin Fiqhu ta kasa da kasa ta OIC don bunkasa hadin guiwa a fannin bincike.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima
Manyan Labarai

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
Manyan Labarai

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Next Post
AFCON 2023: Za A Kece Raini Tsakanin Nijeriya Da Cote de’Voire A Wasan Karshe Ranar Lahadi

Gwamnatin Nijeriya Ta Yaba Da Ƙwazon Tawagar 'Yan Nijeriya A Wasannin Afirka

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

November 1, 2025
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

November 1, 2025
Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.