ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Malaman Musulunci Suna Taro A Makkah Kan Ƙarfafa Samar Da Haɗin Kai A Tsakanin Musulmi

by Muhammad
2 years ago
Musulunci

A ranar Litinin dinnan aka fara gabatar da wani taron kasa da kasa mai taken “Gina Gada tsakanin Mazhabobin Musulunci da Kungiyoyin Musulunci” a birnin Makkah na kasar Saudaiyya.

Taron wanda kungiyar kasashen musulmi ta duniya MWL ta shirya kuma Sarki Salman bin Abdulaziz ya dauki nauyin taron, ya samu halartar wakilai da dama na mabiya addinin Islama. Malamai sun bayyana aniyarsu ta inganta al’amura gama gari don farfado da gudummawar da al’ummar Musulmi ke bayarwa wajen wayar da kai da samar da ci gaba.

  • Sakamakon Taron Kasashen Musulmi Da Larabawa: Saudiyya Da Nijeriya Za Su Jagoranci ‘Yantar Da Falasdin
  • Samar Da Jami’ar Musulunci A Jihar Kaduna Alheri Ne – Bola Ige

Shugaban kungiyar MWL, Mohammed Al-Issa l, ya sanar da shirin kaddamar da daftarin aiki da ke bayyana muhimman ka’idojin samar da hadin kai a tsakanin kungiyoyin Musulunci don tunkarar kalubale yadda ya kamata.

ADVERTISEMENT

Al-Issa ya kuma bayyana irin farin cikinsa da karbar bakuncin taron mai dimbin tarihi a Makkah tare da jaddada bukatar hadin kan al’ummar Musulmi.

Al-Issa ya yi gargadi game da kalaman bangaranci, ya kuma yi kira da a rika yada labaran da suka dace a kafafen yada labarai da ke kara samar da hadin kai. Daga nan sai ya mika godiyarsa ga mahukuntan kasar Saudiyya kan goyon bayan da suke ba shi, ya kuma yi addu’ar Allah ya kara masa lafiya.

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

An fara taron ya samu kyakkyawar tarba daga babban Mufti na Saudiyya, Sheikh Abdulaziz Al-Sheikh, wanda Dr. Fahd Al-Majid ya gabatar.

Al-Sheikh ya jaddada muhimmancin hadin kai a Musulunci, ya kuma yi gargadi kan illar rarrabuwar kawuna tare da bayyana irin rawar da malamai ke takawa wajen samar da hadin kai a tsakanin musulmi.

Ya godewa mai kula da masallatai masu alfarma guda biyu, Sarki Salman bin Abdulaziz kan goyon bayan taron tare da yabawa kokarin hadin kan musulmi, karkashin jagorancin Yarima Mohammed bin Salman, Yarima mai jiran gado kuma Firayim Ministan Saudiyya.

An mika godiya ga wadanda suka shirya taron, wanda MWL ya wakilta, saboda hidimar da suke ci gaba da yi wa Musulunci da Musulmai.

Hissein Brahim Taha, babban sakataren kungiyar hadin kan kasashen musulmi OIC, ya yabawa sarki Salman da yarima mai jiran gado Mohammed bisa goyon bayan taron.

Ya yi bayani cewa muhimmin taron zai inganta hadin kai a tsakanin mazhabobin Musulunci, tare da shawarwarin da za a yi amfani da su wajen samar da hadin kai da magance sabani.

Taha ya kuma yabawa kungiyar MWL bisa sadaukarwar da take yi wa Musulunci da Musulmin duniya.

A gefe guda kuma, an sanya hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna tsakanin MWL da OIC kan hadin kai a tsakanin Kungiyoyin biyu.

An rattaba hannu kan wata yarjejeniya tsakanin Cibiyar Fiqhu ta Musulunci ta MWL da Cibiyar Nazarin Fiqhu ta kasa da kasa ta OIC don bunkasa hadin guiwa a fannin bincike.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC
Manyan Labarai

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025
NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama
Manyan Labarai

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama

November 15, 2025
Next Post
AFCON 2023: Za A Kece Raini Tsakanin Nijeriya Da Cote de’Voire A Wasan Karshe Ranar Lahadi

Gwamnatin Nijeriya Ta Yaba Da Ƙwazon Tawagar 'Yan Nijeriya A Wasannin Afirka

LABARAI MASU NASABA

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025
Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

November 15, 2025
Za A Yi Gwanjon Rigunan Messi Na Gasar Kofin Duniya Ta 2022 Da Kudi Tsagwagwa

Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi

November 15, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

November 15, 2025
Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

November 15, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

November 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

November 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.