ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Malaman Musulunci Suna Taro A Makkah Kan Ƙarfafa Samar Da Haɗin Kai A Tsakanin Musulmi

by Muhammad
2 years ago
Musulunci

A ranar Litinin dinnan aka fara gabatar da wani taron kasa da kasa mai taken “Gina Gada tsakanin Mazhabobin Musulunci da Kungiyoyin Musulunci” a birnin Makkah na kasar Saudaiyya.

Taron wanda kungiyar kasashen musulmi ta duniya MWL ta shirya kuma Sarki Salman bin Abdulaziz ya dauki nauyin taron, ya samu halartar wakilai da dama na mabiya addinin Islama. Malamai sun bayyana aniyarsu ta inganta al’amura gama gari don farfado da gudummawar da al’ummar Musulmi ke bayarwa wajen wayar da kai da samar da ci gaba.

  • Sakamakon Taron Kasashen Musulmi Da Larabawa: Saudiyya Da Nijeriya Za Su Jagoranci ‘Yantar Da Falasdin
  • Samar Da Jami’ar Musulunci A Jihar Kaduna Alheri Ne – Bola Ige

Shugaban kungiyar MWL, Mohammed Al-Issa l, ya sanar da shirin kaddamar da daftarin aiki da ke bayyana muhimman ka’idojin samar da hadin kai a tsakanin kungiyoyin Musulunci don tunkarar kalubale yadda ya kamata.

ADVERTISEMENT

Al-Issa ya kuma bayyana irin farin cikinsa da karbar bakuncin taron mai dimbin tarihi a Makkah tare da jaddada bukatar hadin kan al’ummar Musulmi.

Al-Issa ya yi gargadi game da kalaman bangaranci, ya kuma yi kira da a rika yada labaran da suka dace a kafafen yada labarai da ke kara samar da hadin kai. Daga nan sai ya mika godiyarsa ga mahukuntan kasar Saudiyya kan goyon bayan da suke ba shi, ya kuma yi addu’ar Allah ya kara masa lafiya.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

An fara taron ya samu kyakkyawar tarba daga babban Mufti na Saudiyya, Sheikh Abdulaziz Al-Sheikh, wanda Dr. Fahd Al-Majid ya gabatar.

Al-Sheikh ya jaddada muhimmancin hadin kai a Musulunci, ya kuma yi gargadi kan illar rarrabuwar kawuna tare da bayyana irin rawar da malamai ke takawa wajen samar da hadin kai a tsakanin musulmi.

Ya godewa mai kula da masallatai masu alfarma guda biyu, Sarki Salman bin Abdulaziz kan goyon bayan taron tare da yabawa kokarin hadin kan musulmi, karkashin jagorancin Yarima Mohammed bin Salman, Yarima mai jiran gado kuma Firayim Ministan Saudiyya.

An mika godiya ga wadanda suka shirya taron, wanda MWL ya wakilta, saboda hidimar da suke ci gaba da yi wa Musulunci da Musulmai.

Hissein Brahim Taha, babban sakataren kungiyar hadin kan kasashen musulmi OIC, ya yabawa sarki Salman da yarima mai jiran gado Mohammed bisa goyon bayan taron.

Ya yi bayani cewa muhimmin taron zai inganta hadin kai a tsakanin mazhabobin Musulunci, tare da shawarwarin da za a yi amfani da su wajen samar da hadin kai da magance sabani.

Taha ya kuma yabawa kungiyar MWL bisa sadaukarwar da take yi wa Musulunci da Musulmin duniya.

A gefe guda kuma, an sanya hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna tsakanin MWL da OIC kan hadin kai a tsakanin Kungiyoyin biyu.

An rattaba hannu kan wata yarjejeniya tsakanin Cibiyar Fiqhu ta Musulunci ta MWL da Cibiyar Nazarin Fiqhu ta kasa da kasa ta OIC don bunkasa hadin guiwa a fannin bincike.

Musulunci
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
AFCON 2023: Za A Kece Raini Tsakanin Nijeriya Da Cote de’Voire A Wasan Karshe Ranar Lahadi

Gwamnatin Nijeriya Ta Yaba Da Ƙwazon Tawagar 'Yan Nijeriya A Wasannin Afirka

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.