ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Malamar Jami’ar Nasarawa Da Aka Sace Ta Kubuta

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Nasarawa

Malamar jami’ar jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK), Dakta Comfort Adokwe, da aka yi garkuwa da ita, ta kubuta daga hannun masu garkuwa da mutane bayan shafe kwanaki uku a hannunsu.

Dakta Adokwe dai ta samu kubuta ne a daren ranar Talata bayan biyan kudin fansa naira miliyan biyar da iyalanta suka biya, kamar yadda wakilinmu ya gano a ranar Laraba.

  • Tinubu Ya Nada Kwamishinonin INEC A Jihohi 9
  • UNESCO Ta Yi Bikin Ranar Amfani Da Kafofin Watsa Labarai Da Yada Bayanai Ta Duniya A Abuja

Idan za a tuna, Dakta Adokwe, wacce malama ce a tsangayar nazarin mulki kuma mataimakiyar daraktan darusan jinsi, an yi garkuwa da ita ne a gidanta da ke Angwan Jaba a cikin garin Keffi a daren ranar Lahadi.

ADVERTISEMENT

An nakalto cewa ‘yan bindigan sun yi ta harbe-harbe a sama lokacin da suka je gidan matar daga bisani suka yi awun gaba da ita.

LEADERSHIP tun da farko ta labarto cewa masu garkuwan sun nemi kudin fansa naira miliyan 15 kafin su sake ta, amma iyalanta sun nuna cewa wannan kudin ya musu yawa ba za su iya biyan hakan ba.

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Daya daga cikin iyalanta, Mista Timothy Adokwe, ya shaida wa ‘yan jarida cewar an sako malamar da karfe 10 na daren ranar Talata bayan da aka biya kudin fansa.

Ya ce, daya daga cikin ahlin malamar ne ya kai kudin zuwa inda masu garkuwan suka umarta daga bisani suka sako ta.

Ya kara da cewa hukumomin tsaro sun yi iyaka nasu kokarin wajen bibiyar masu garkuwan, amma an dakile aniyarsu domin tabbatar da cewa ba a jefa rayuwar malamar cikin hadari ba.

“Mun fi damuwa kan yadda za mu kare ‘yar uwanmu. Jami’an tsaro sun yi iyaka kokarinsu, sun taimaka wajen bibiyar sawun masu garkuwan.

“Amma bisa gargadin da masu garkuwan suka yi na cewa muddin aka yi wani motsi to za su kasheta, hakan ya sa muka roki jami’an tsaron da kada su yi wani abu domin tabbatar da lafiyarta.

“Ina sane da cewa hukumomin tsaron sun bibiya dukkanin abubuwan da suka faru kila za su bibiyi sawun masu garkuwan.

“Muna godiya wa kowa da kowa bisa taimako har zuwa lokacin dawowar ‘yar uwan namu,” ya shaida.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Next Post
Jakadan Sin Mai Kula Da Shirin Kwance Damarar Makamai Ya Yi Kira Da A Tabbatar Da Ikon Kasashe Masu Tasowa Na Yin Amfani Da Kimiyya Da Fasaha Cikin Lumana

Jakadan Sin Mai Kula Da Shirin Kwance Damarar Makamai Ya Yi Kira Da A Tabbatar Da Ikon Kasashe Masu Tasowa Na Yin Amfani Da Kimiyya Da Fasaha Cikin Lumana

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.