• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Malamar Jami’ar Nasarawa Da Aka Sace Ta Kubuta

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Malamar Jami’ar Nasarawa Da Aka Sace Ta Kubuta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Malamar jami’ar jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK), Dakta Comfort Adokwe, da aka yi garkuwa da ita, ta kubuta daga hannun masu garkuwa da mutane bayan shafe kwanaki uku a hannunsu.

Dakta Adokwe dai ta samu kubuta ne a daren ranar Talata bayan biyan kudin fansa naira miliyan biyar da iyalanta suka biya, kamar yadda wakilinmu ya gano a ranar Laraba.

  • Tinubu Ya Nada Kwamishinonin INEC A Jihohi 9
  • UNESCO Ta Yi Bikin Ranar Amfani Da Kafofin Watsa Labarai Da Yada Bayanai Ta Duniya A Abuja

Idan za a tuna, Dakta Adokwe, wacce malama ce a tsangayar nazarin mulki kuma mataimakiyar daraktan darusan jinsi, an yi garkuwa da ita ne a gidanta da ke Angwan Jaba a cikin garin Keffi a daren ranar Lahadi.

An nakalto cewa ‘yan bindigan sun yi ta harbe-harbe a sama lokacin da suka je gidan matar daga bisani suka yi awun gaba da ita.

LEADERSHIP tun da farko ta labarto cewa masu garkuwan sun nemi kudin fansa naira miliyan 15 kafin su sake ta, amma iyalanta sun nuna cewa wannan kudin ya musu yawa ba za su iya biyan hakan ba.

Labarai Masu Nasaba

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Daya daga cikin iyalanta, Mista Timothy Adokwe, ya shaida wa ‘yan jarida cewar an sako malamar da karfe 10 na daren ranar Talata bayan da aka biya kudin fansa.

Ya ce, daya daga cikin ahlin malamar ne ya kai kudin zuwa inda masu garkuwan suka umarta daga bisani suka sako ta.

Ya kara da cewa hukumomin tsaro sun yi iyaka nasu kokarin wajen bibiyar masu garkuwan, amma an dakile aniyarsu domin tabbatar da cewa ba a jefa rayuwar malamar cikin hadari ba.

“Mun fi damuwa kan yadda za mu kare ‘yar uwanmu. Jami’an tsaro sun yi iyaka kokarinsu, sun taimaka wajen bibiyar sawun masu garkuwan.

“Amma bisa gargadin da masu garkuwan suka yi na cewa muddin aka yi wani motsi to za su kasheta, hakan ya sa muka roki jami’an tsaron da kada su yi wani abu domin tabbatar da lafiyarta.

“Ina sane da cewa hukumomin tsaron sun bibiya dukkanin abubuwan da suka faru kila za su bibiyi sawun masu garkuwan.

“Muna godiya wa kowa da kowa bisa taimako har zuwa lokacin dawowar ‘yar uwan namu,” ya shaida.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Amurka Ce Ke Rura Wutar Rikici A Tsakanin Palasdinu Da Isra’ila

Next Post

Jakadan Sin Mai Kula Da Shirin Kwance Damarar Makamai Ya Yi Kira Da A Tabbatar Da Ikon Kasashe Masu Tasowa Na Yin Amfani Da Kimiyya Da Fasaha Cikin Lumana

Related

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

2 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

3 hours ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

3 hours ago
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

8 hours ago
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
Manyan Labarai

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

20 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

22 hours ago
Next Post
Jakadan Sin Mai Kula Da Shirin Kwance Damarar Makamai Ya Yi Kira Da A Tabbatar Da Ikon Kasashe Masu Tasowa Na Yin Amfani Da Kimiyya Da Fasaha Cikin Lumana

Jakadan Sin Mai Kula Da Shirin Kwance Damarar Makamai Ya Yi Kira Da A Tabbatar Da Ikon Kasashe Masu Tasowa Na Yin Amfani Da Kimiyya Da Fasaha Cikin Lumana

LABARAI MASU NASABA

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

June 28, 2025
Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

June 28, 2025
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

June 28, 2025
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

June 28, 2025
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

June 28, 2025
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

June 28, 2025
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

June 28, 2025
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.