• English
  • Business News
Monday, October 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Malamar Jami’ar Nasarawa Da Aka Sace Ta Kubuta

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Nasarawa

Malamar jami’ar jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK), Dakta Comfort Adokwe, da aka yi garkuwa da ita, ta kubuta daga hannun masu garkuwa da mutane bayan shafe kwanaki uku a hannunsu.

Dakta Adokwe dai ta samu kubuta ne a daren ranar Talata bayan biyan kudin fansa naira miliyan biyar da iyalanta suka biya, kamar yadda wakilinmu ya gano a ranar Laraba.

  • Tinubu Ya Nada Kwamishinonin INEC A Jihohi 9
  • UNESCO Ta Yi Bikin Ranar Amfani Da Kafofin Watsa Labarai Da Yada Bayanai Ta Duniya A Abuja

Idan za a tuna, Dakta Adokwe, wacce malama ce a tsangayar nazarin mulki kuma mataimakiyar daraktan darusan jinsi, an yi garkuwa da ita ne a gidanta da ke Angwan Jaba a cikin garin Keffi a daren ranar Lahadi.

An nakalto cewa ‘yan bindigan sun yi ta harbe-harbe a sama lokacin da suka je gidan matar daga bisani suka yi awun gaba da ita.

LEADERSHIP tun da farko ta labarto cewa masu garkuwan sun nemi kudin fansa naira miliyan 15 kafin su sake ta, amma iyalanta sun nuna cewa wannan kudin ya musu yawa ba za su iya biyan hakan ba.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

Daya daga cikin iyalanta, Mista Timothy Adokwe, ya shaida wa ‘yan jarida cewar an sako malamar da karfe 10 na daren ranar Talata bayan da aka biya kudin fansa.

Ya ce, daya daga cikin ahlin malamar ne ya kai kudin zuwa inda masu garkuwan suka umarta daga bisani suka sako ta.

Ya kara da cewa hukumomin tsaro sun yi iyaka nasu kokarin wajen bibiyar masu garkuwan, amma an dakile aniyarsu domin tabbatar da cewa ba a jefa rayuwar malamar cikin hadari ba.

“Mun fi damuwa kan yadda za mu kare ‘yar uwanmu. Jami’an tsaro sun yi iyaka kokarinsu, sun taimaka wajen bibiyar sawun masu garkuwan.

“Amma bisa gargadin da masu garkuwan suka yi na cewa muddin aka yi wani motsi to za su kasheta, hakan ya sa muka roki jami’an tsaron da kada su yi wani abu domin tabbatar da lafiyarta.

“Ina sane da cewa hukumomin tsaron sun bibiya dukkanin abubuwan da suka faru kila za su bibiyi sawun masu garkuwan.

“Muna godiya wa kowa da kowa bisa taimako har zuwa lokacin dawowar ‘yar uwan namu,” ya shaida.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno

October 27, 2025
Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum
Manyan Labarai

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

October 26, 2025
“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”
Labarai

“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

October 26, 2025
Next Post
Jakadan Sin Mai Kula Da Shirin Kwance Damarar Makamai Ya Yi Kira Da A Tabbatar Da Ikon Kasashe Masu Tasowa Na Yin Amfani Da Kimiyya Da Fasaha Cikin Lumana

Jakadan Sin Mai Kula Da Shirin Kwance Damarar Makamai Ya Yi Kira Da A Tabbatar Da Ikon Kasashe Masu Tasowa Na Yin Amfani Da Kimiyya Da Fasaha Cikin Lumana

LABARAI MASU NASABA

Nasarawa

Tsohon Gwamnan Jigawa, Lamido Ya Bayyana Aniyar Takarar Shugabancin Jam’iyyar PDP Na Ƙasa

October 27, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno

October 27, 2025
Hatsarin Jiragen Ruwa

Matasa 5 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Gombe

October 27, 2025
Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

October 26, 2025
Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

October 26, 2025
Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya

Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya

October 26, 2025
“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

October 26, 2025
Ya Zuwa Satumban Bana Adadin Lantarki Da Sin Ta Samar Ya Karu Da Kaso 17.5%

Ya Zuwa Satumban Bana Adadin Lantarki Da Sin Ta Samar Ya Karu Da Kaso 17.5%

October 26, 2025
Dalilin Da Suka Sa Hisbah Ta Dakatar Da Auren Ƴan TikTok A Kano

Dalilin Da Suka Sa Hisbah Ta Dakatar Da Auren Ƴan TikTok A Kano

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati Na Shekarar 2025, Dakta Zacch Adedeji

October 26, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.