• English
  • Business News
Tuesday, October 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mambobin ASUU A Bauchi Sun Yi Zanga-zanga Kan Bukatunsu 

Sun Yi Tir Da Matakin Sayar Da Jami'o'i Da Fatali Da Tsarin IPPIS

byKhalid Idris Doya
3 years ago
inManyan Labarai
0
ASUU

Mambobin Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), a Jihar Bauchi, sun gudanar da zanga-zangar lumana a ranar Talata domin shaida wa duniya cewa har zuwa yanzu Gwamnatin tarayya ta kasa cimma bukatun da suke da su tare da neman yanayin koyarwa mai inganci.

Shiyyar ASUU na Bauchi ya kunshi jami’o’in Bauchi, Gombe, da jihar Filato sun yi zanga-zangar ne a Bauchi inda suka fito daga cikin jami’ar ATBU tare da fitowa kan titi na mintuna dauke da takardun da suke alamta bukatunsu daban-daban gami da yin wakokin neman goyon baya.

  • Jaruman Nollywood Da Kannywood Sun Yi Wa Jos Tsinke Don Mara Wa Tinubu Baya 
  • Yawan Adadin Mutane A Fadin Duniya Ya Doshi Mutum Biliyan 8 — MDD

Da ya ke ganawa da ‘yan jarida, Shugaban kungiyar ASUU a jami’ar ATBU, Dakta Ibrahim Ibrahim Inuwa ya roki masu ruwa da tsaki a Nijeriya da su matsa wa Gwamnatin tarayya lamba wajen ganin ta cika dukkkanin bukatun Malaman jami’o’i domin tabbatar da ci gaban kasa da inganta harkokin ilimi.

Ya ce, dole ne su yi tsawa su yi tsayin daka wajen kare tsarin jami’o’i a kasar nan ta hanyar bin matakan da doka suka shimfida.

Kazalika, ASUU din ta yi tir gami da fatali da kokarin gwamnati na sayar da jami’o’in kasar nan.

Labarai Masu Nasaba

Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Rage Kuɗin Aikin Hajjin 2026

Dakta Ibrahim ya ce tun lokacin da suka janye yajin aikin watanni 8 sakamakon umarnin kotu da bukatar wasu ‘yan Nijeriya, Gwamnatin tarayya take sako-sako da batun biya musu bukatunsu a maimakon haka ma sai biyansu albashin watan Oktoba ta yi ba yadda ya dace ba.

Ya kara da cewa da gangan wasu ke nacewa wajen maida jami’o’i zuwa masu zaman kansu domin wasu daidaiku ne ke amfana da jami’o’i masu zaman kansu kuma hakan ba zai taimaka wa talakawa kasa wajen samun ilimi cikin sauki ba.

ASUU ta kara da nuna damuwarta kan cewa bisa fito da tsarin biyan albashi ta IPPIS wasu hakkokinsu da dama da doka ya ware musu an danne musu kuma ba za su lamunce da hakan ba.

Kungiyar dai ya ce tana da tulin bukatun da suke son Gwamnatin tarayya ta cimma musu amma har yanzu yanzu ba su ga sakamakon mai kyau ba. Don haka ne suka nemi masu ruwa da tsaki da fa su sanya baki domin ganin an shawo kan matsalolin.

Har-ila-yau, sun ce basu son sake shiga yajin aiki a Nan kusa domin cigaban amsa amma ba za su zura ido Kuma ana zalumtaersu ba, don haka ne a cewarsu suka dauki matakin yin zanga-zanga domin nuna wa duniya cewa har yanzu yanzu Gwamnatin tarayya ba ta shirya wa kawo karshen matsalolin da malaman jami’o’i ke fama da su ba.

Tags: ASUUBauchiGwamnatin TarayyaIlimiTakaddamaYajin AikiZanga-zanga
ShareTweetSendShare
Khalid Idris Doya

Khalid Idris Doya

Related

Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa
Manyan Labarai

Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa

4 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Rage Kuɗin Aikin Hajjin 2026

5 hours ago
Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 
Manyan Labarai

Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 

17 hours ago
Next Post

Xi Jinping: Sin Na Goyon Bayan Shigar Da Kungiyar AU G20

LABARAI MASU NASABA

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

October 7, 2025
Tsaro: Gwamnan Kogi Ya Ayyana Yaƙi Da Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba Da ‘Yan Bindiga

Tsaro: Gwamnan Kogi Ya Ayyana Yaƙi Da Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba Da ‘Yan Bindiga

October 7, 2025
Majalisar Wakilai Ta Kafa Kwamiti Da Zai Binciki Harkokin Kirifto Da POS A Nijeriya

Majalisar Wakilai Ta Kafa Kwamiti Da Zai Binciki Harkokin Kirifto Da POS A Nijeriya

October 7, 2025
Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa

Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa

October 7, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Rage Kuɗin Aikin Hajjin 2026

October 7, 2025
Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

October 6, 2025
Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 

Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 

October 6, 2025
Habakar Yin Sayayya A Lokacin Hutu Ta Nuna Kirkira Da Irin Ci Gaban Da Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samu   

Habakar Yin Sayayya A Lokacin Hutu Ta Nuna Kirkira Da Irin Ci Gaban Da Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samu   

October 6, 2025
Karamin Ofishin Jakadancin Sin Da Ke Legas Ya Yi Bikin Bunkasa Al’adu Na Bikin Tsakiyar Kaka

Karamin Ofishin Jakadancin Sin Da Ke Legas Ya Yi Bikin Bunkasa Al’adu Na Bikin Tsakiyar Kaka

October 6, 2025
Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

October 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.